< Ayuba 3 >

1 Bayan wannan Ayuba ya buɗe baki ya la’anta ranar da aka haife shi.
Alors Job ouvrit la bouche et maudit le jour de sa naissance.
2 Ayuba ya ce,
Job prit la parole et dit:
3 “A hallaka ranar da aka haife ni, da kuma daren da aka ce, ‘An haifi jariri namiji!’
Périsse le jour où je suis né, et la nuit qui a dit: « Un homme est conçu! »
4 Bari ranan nan ta zama duhu; kada Allah yă kula da ita; kada rana tă yi haske a wannan rana.
Ce jour, qu’il se change en ténèbres, que Dieu d’en haut n’en ait pas souci, que la lumière ne brille pas sur lui!
5 Bari duhu da inuwa mai duhu ta sāke rufe ta; gizagizai kuma su rufe ta; duhu kuma ya rufe haskenta.
Que les ténèbres et l’ombre de la mort le revendiquent, qu’un nuage épais le couvre, que l’éclipse de sa lumière jette l’épouvante!
6 Bari duhu mai yawa yă rufe daren nan; kada a haɗa ta cikin kwanakin shekara, ko kuma cikin kwanakin watanni.
Cette nuit, que les ténèbres en fassent leur proie, qu’elle ne compte pas dans les jours de l’année, qu’elle n’entre pas dans la supputation des mois!
7 Bari daren yă zama marar amfani; kada a ji wata sowa ta farin ciki.
Que cette nuit soit un désert stérile, qu’on n’y entende pas de cri d’allégresse!
8 Bari waɗanda suke la’anta ranaku su la’anta wannan rana su waɗanda suke umartar dodon ruwa.
Que ceux-là la maudissent, qui maudissent les jours, qui savent évoquer Léviathan!
9 Bari taurarinta na safe su zama duhu; bari ranar tă yi ta jiran ganin haske amma kada tă gani,
Que les étoiles de son crépuscule s’obscurcissent, qu’elle attende la lumière, sans qu’elle vienne, et qu’elle ne voie pas les paupières de l’aurore,
10 gama ba tă hana uwata ɗaukar cikina, don ta hana ni shan wahalan nan ba.
parce qu’elle ne m’a pas fermé les portes du sein, et n’a pas dérobé la souffrance à mes regards!
11 “Me ya sa ban mutu ba da za a haife ni, ko kuma in mutu sa’ad da ana haihuwata ba?
Que ne suis-je mort dès le ventre de ma mère, au sortir de ses entrailles que n’ai-je expiré!
12 Me ya sa aka haife ni, aka tanada nono na sha na rayu?
Pourquoi ai-je trouvé deux genoux pour me recevoir, et pourquoi deux mamelles à sucer?
13 Da yanzu ina kwance cikin salama; da ina barcina cikin salama
Maintenant je serais couché et en paix, je dormirais et je me reposerais
14 tare da sarakuna da mashawarta a cikin ƙasa, waɗanda suka gina wa kansu wuraren da yanzu duk sun rushe,
avec les rois et les grands de la terre, qui se sont bâti des mausolées;
15 da shugabanni waɗanda suke da zinariya, waɗanda suka cika gidajensu da azurfa.
avec les princes qui avaient de l’or, et remplissaient d’argent leur demeures.
16 Ko kuma don me ba a ɓoye ni a cikin ƙasa kamar jaririn da aka haifa ba rai ba, kamar jaririn da bai taɓa ganin hasken rana ba.
Ou bien, comme l’avorton ignoré, je n’existerais pas, comme ces enfants qui n’ont pas vu la lumière.
17 A wurin mugaye za su daina yin mugunta, gajiyayyu kuma za su huta.
Là les méchants n’exercent plus leurs violences, là se repose l’homme épuisé de forces;
18 Waɗanda aka daure za su sami jin daɗin; an sake su ba za su sāke jin ana tsawata masu ba.
les captifs y sont tous en paix, ils n’entendent plus la voix de l’exacteur.
19 Manyan da ƙanana suna a can, bawa kuma ya sami’yanci daga wurin maigidansa.
Là se trouvent le petit et le grand, l’esclave affranchi de son maître.
20 “Don me ake ba da haske ga waɗanda suke cikin ƙunci, rai kuma ga masu ɗacin rai
Pourquoi donner la lumière aux malheureux, et la vie à ceux dont l’âme est remplie d’amertume,
21 ga waɗanda suke neman mutuwa amma ba su samu ba, waɗanda suke nemanta kamar wani abu mai daraja a ɓoye,
qui espèrent la mort, et la mort ne vient pas, qui la cherchent plus ardemment que les trésors,
22 waɗanda suke farin ciki sa’ad da suka kai kabari?
qui sont heureux, qui tressaillent d’aise et se réjouissent quand ils ont trouvé le tombeau;
23 Don me aka ba mutum rai, mutumin da bai san wani abu game da kansa ba, mutumin da Allah ya kange shi.
à l’homme dont la route est cachée et que Dieu enferme de toutes parts?
24 Baƙin ciki ya ishe ni maimakon abinci; ina ta yin nishi ba fasawa;
Mes soupirs sont comme mon pain et mes gémissements se répandent comme l’eau.
25 Abin da nake tsoro ya faru da ni; abin da ba na so ya same ni.
Ce que je crains, c’est ce qui m’arrive; ce que je redoute fond sur moi.
26 Ba ni da salama, ba natsuwa; ba ni da hutu, sai wahala kawai.”
Plus de tranquillité, plus de paix, plus de repos, et le trouble m’a saisi.

< Ayuba 3 >