< Ayuba 3 >

1 Bayan wannan Ayuba ya buɗe baki ya la’anta ranar da aka haife shi.
After this hath Job opened his mouth, and revileth his day.
2 Ayuba ya ce,
And Job answereth and saith: —
3 “A hallaka ranar da aka haife ni, da kuma daren da aka ce, ‘An haifi jariri namiji!’
Let the day perish in which I am born, And the night that hath said: 'A man-child hath been conceived.'
4 Bari ranan nan ta zama duhu; kada Allah yă kula da ita; kada rana tă yi haske a wannan rana.
That day — let it be darkness, Let not God require it from above, Nor let light shine upon it.
5 Bari duhu da inuwa mai duhu ta sāke rufe ta; gizagizai kuma su rufe ta; duhu kuma ya rufe haskenta.
Let darkness and death-shade redeem it, Let a cloud tabernacle upon it, Let them terrify it as the most bitter of days.
6 Bari duhu mai yawa yă rufe daren nan; kada a haɗa ta cikin kwanakin shekara, ko kuma cikin kwanakin watanni.
That night — let thick darkness take it, Let it not be united to days of the year, Into the number of months let it not come.
7 Bari daren yă zama marar amfani; kada a ji wata sowa ta farin ciki.
Lo! that night — let it be gloomy, Let no singing come into it.
8 Bari waɗanda suke la’anta ranaku su la’anta wannan rana su waɗanda suke umartar dodon ruwa.
Let the cursers of day mark it, Who are ready to wake up Leviathan.
9 Bari taurarinta na safe su zama duhu; bari ranar tă yi ta jiran ganin haske amma kada tă gani,
Let the stars of its twilight be dark, Let it wait for light, and there is none, And let it not look on the eyelids of the dawn.
10 gama ba tă hana uwata ɗaukar cikina, don ta hana ni shan wahalan nan ba.
Because it hath not shut the doors Of the womb that was mine! And hide misery from mine eyes.
11 “Me ya sa ban mutu ba da za a haife ni, ko kuma in mutu sa’ad da ana haihuwata ba?
Why from the womb do I not die? From the belly I have come forth and gasp!
12 Me ya sa aka haife ni, aka tanada nono na sha na rayu?
Wherefore have knees been before me? And what [are] breasts, that I suck?
13 Da yanzu ina kwance cikin salama; da ina barcina cikin salama
For now, I have lain down, and am quiet, I have slept — then there is rest to me,
14 tare da sarakuna da mashawarta a cikin ƙasa, waɗanda suka gina wa kansu wuraren da yanzu duk sun rushe,
With kings and counsellors of earth, These building wastes for themselves.
15 da shugabanni waɗanda suke da zinariya, waɗanda suka cika gidajensu da azurfa.
Or with princes — they have gold, They are filling their houses [with] silver.
16 Ko kuma don me ba a ɓoye ni a cikin ƙasa kamar jaririn da aka haifa ba rai ba, kamar jaririn da bai taɓa ganin hasken rana ba.
(Or as a hidden abortion I am not, As infants — they have not seen light.)
17 A wurin mugaye za su daina yin mugunta, gajiyayyu kuma za su huta.
There the wicked have ceased troubling, And there rest do the wearied in power.
18 Waɗanda aka daure za su sami jin daɗin; an sake su ba za su sāke jin ana tsawata masu ba.
Together prisoners have been at ease, They have not heard the voice of an exactor,
19 Manyan da ƙanana suna a can, bawa kuma ya sami’yanci daga wurin maigidansa.
Small and great [are] there the same. And a servant [is] free from his lord.
20 “Don me ake ba da haske ga waɗanda suke cikin ƙunci, rai kuma ga masu ɗacin rai
Why giveth He to the miserable light, and life to the bitter soul?
21 ga waɗanda suke neman mutuwa amma ba su samu ba, waɗanda suke nemanta kamar wani abu mai daraja a ɓoye,
Who are waiting for death, and it is not, And they seek it above hid treasures.
22 waɗanda suke farin ciki sa’ad da suka kai kabari?
Who are glad — unto joy, They rejoice when they find a grave.
23 Don me aka ba mutum rai, mutumin da bai san wani abu game da kansa ba, mutumin da Allah ya kange shi.
To a man whose way hath been hidden, And whom God doth shut up?
24 Baƙin ciki ya ishe ni maimakon abinci; ina ta yin nishi ba fasawa;
For before my food, my sighing cometh, And poured out as waters [are] my roarings.
25 Abin da nake tsoro ya faru da ni; abin da ba na so ya same ni.
For a fear I feared and it meeteth me, And what I was afraid of doth come to me.
26 Ba ni da salama, ba natsuwa; ba ni da hutu, sai wahala kawai.”
I was not safe — nor was I quiet — Nor was I at rest — and trouble cometh!

< Ayuba 3 >