< Ayuba 3 >
1 Bayan wannan Ayuba ya buɗe baki ya la’anta ranar da aka haife shi.
After this Job opened his mouth, and cursed his day.
3 “A hallaka ranar da aka haife ni, da kuma daren da aka ce, ‘An haifi jariri namiji!’
Let the day perish in which I was born, and the night [in which] it was said, There is a man child conceived.
4 Bari ranan nan ta zama duhu; kada Allah yă kula da ita; kada rana tă yi haske a wannan rana.
Let that day be darkness; let not God regard it from above, neither let the light shine upon it.
5 Bari duhu da inuwa mai duhu ta sāke rufe ta; gizagizai kuma su rufe ta; duhu kuma ya rufe haskenta.
Let darkness and the shades of death stain it; let a cloud dwell upon it; let the blackness of the day terrify it.
6 Bari duhu mai yawa yă rufe daren nan; kada a haɗa ta cikin kwanakin shekara, ko kuma cikin kwanakin watanni.
As [for] that night, let darkness seize upon it; let it not be joined to the days of the year, let it not come into the number of the months.
7 Bari daren yă zama marar amfani; kada a ji wata sowa ta farin ciki.
Lo, let that night be solitary, let no joyful voice come therein.
8 Bari waɗanda suke la’anta ranaku su la’anta wannan rana su waɗanda suke umartar dodon ruwa.
Let them curse it that curse the day, who are ready to raise up their mourning.
9 Bari taurarinta na safe su zama duhu; bari ranar tă yi ta jiran ganin haske amma kada tă gani,
Let the stars of its twilight be dark; let it look for light, but [have] none; neither let it see the dawning of the day:
10 gama ba tă hana uwata ɗaukar cikina, don ta hana ni shan wahalan nan ba.
Because it prevented not my birth, nor hid sorrow from my eyes.
11 “Me ya sa ban mutu ba da za a haife ni, ko kuma in mutu sa’ad da ana haihuwata ba?
Why died I not from the womb? [why] did I [not] expire at the time of my birth?
12 Me ya sa aka haife ni, aka tanada nono na sha na rayu?
Why did the knees receive me? or why the breasts that I should be nursed?
13 Da yanzu ina kwance cikin salama; da ina barcina cikin salama
For now should I have lain still and been quiet, I should have slept: then had I been at rest,
14 tare da sarakuna da mashawarta a cikin ƙasa, waɗanda suka gina wa kansu wuraren da yanzu duk sun rushe,
With kings and counselors of the earth, who built desolate places for themselves;
15 da shugabanni waɗanda suke da zinariya, waɗanda suka cika gidajensu da azurfa.
Or with princes that had gold, who filled their houses with silver:
16 Ko kuma don me ba a ɓoye ni a cikin ƙasa kamar jaririn da aka haifa ba rai ba, kamar jaririn da bai taɓa ganin hasken rana ba.
Or as a hidden untimely birth I had not been; as infants [which] never saw light.
17 A wurin mugaye za su daina yin mugunta, gajiyayyu kuma za su huta.
There the wicked cease [from] troubling; and there the weary are at rest.
18 Waɗanda aka daure za su sami jin daɗin; an sake su ba za su sāke jin ana tsawata masu ba.
[There] the prisoners rest together; they hear not the voice of the oppressor.
19 Manyan da ƙanana suna a can, bawa kuma ya sami’yanci daga wurin maigidansa.
The small and great are there; and the servant [is] free from his master.
20 “Don me ake ba da haske ga waɗanda suke cikin ƙunci, rai kuma ga masu ɗacin rai
Why is light given to him that is in misery, and life to the bitter [in] soul;
21 ga waɗanda suke neman mutuwa amma ba su samu ba, waɗanda suke nemanta kamar wani abu mai daraja a ɓoye,
Who long for death, but it [cometh] not; and dig for it more than for hid treasures;
22 waɗanda suke farin ciki sa’ad da suka kai kabari?
Who rejoice exceedingly, [and] are glad, when they can find the grave?
23 Don me aka ba mutum rai, mutumin da bai san wani abu game da kansa ba, mutumin da Allah ya kange shi.
[Why is light given] to a man whose way is hid, and whom God hath hedged in?
24 Baƙin ciki ya ishe ni maimakon abinci; ina ta yin nishi ba fasawa;
For my sighing cometh before I eat, and my roarings are poured out like the waters.
25 Abin da nake tsoro ya faru da ni; abin da ba na so ya same ni.
For the thing which I greatly feared hath come upon me, and that which I dreaded hath come to me.
26 Ba ni da salama, ba natsuwa; ba ni da hutu, sai wahala kawai.”
I was not in safety, neither had I rest, neither was I quiet; yet trouble came.