< Ayuba 3 >

1 Bayan wannan Ayuba ya buɗe baki ya la’anta ranar da aka haife shi.
After thus he opened Job mouth his and he cursed day his.
2 Ayuba ya ce,
And he answered Job and he said.
3 “A hallaka ranar da aka haife ni, da kuma daren da aka ce, ‘An haifi jariri namiji!’
Let it perish [the] day [which] I was born on it and the night [which] it said he has been conceived a man.
4 Bari ranan nan ta zama duhu; kada Allah yă kula da ita; kada rana tă yi haske a wannan rana.
The day that let it be darkness may not he care for it God above and may not it shine forth on it daylight.
5 Bari duhu da inuwa mai duhu ta sāke rufe ta; gizagizai kuma su rufe ta; duhu kuma ya rufe haskenta.
Let them reclaim it darkness and deep darkness let it settle down over it cloud let them terrify it [the] darkness of day.
6 Bari duhu mai yawa yă rufe daren nan; kada a haɗa ta cikin kwanakin shekara, ko kuma cikin kwanakin watanni.
The night that let it take it darkness may not it rejoice among [the] days of [the] year in [the] number of [the] months may not it come.
7 Bari daren yă zama marar amfani; kada a ji wata sowa ta farin ciki.
There! the night that let it be barren may not it come a cry of joy in it.
8 Bari waɗanda suke la’anta ranaku su la’anta wannan rana su waɗanda suke umartar dodon ruwa.
Let them curse it cursers of a day the [ones] ready to rouse Leviathan.
9 Bari taurarinta na safe su zama duhu; bari ranar tă yi ta jiran ganin haske amma kada tă gani,
Let them grow dark [the] stars of twilight its let it wait for light and not and may not it look on [the] eyelids of dawn.
10 gama ba tă hana uwata ɗaukar cikina, don ta hana ni shan wahalan nan ba.
For not it shut [the] doors of womb my and it hid trouble from eyes my.
11 “Me ya sa ban mutu ba da za a haife ni, ko kuma in mutu sa’ad da ana haihuwata ba?
Why? not from [the] womb did I die from [the] belly I came forth and I may expire?
12 Me ya sa aka haife ni, aka tanada nono na sha na rayu?
Why? did they receive me knees and why? breasts that I will suckle.
13 Da yanzu ina kwance cikin salama; da ina barcina cikin salama
For now I lay down and I may be at peace I slept then - it is at rest to me.
14 tare da sarakuna da mashawarta a cikin ƙasa, waɗanda suka gina wa kansu wuraren da yanzu duk sun rushe,
With kings and counselors of [the] earth the [ones who] rebuilt ruins for themselves.
15 da shugabanni waɗanda suke da zinariya, waɗanda suka cika gidajensu da azurfa.
Or with princes [whom] gold [belonged] to them those [who] filled houses their silver.
16 Ko kuma don me ba a ɓoye ni a cikin ƙasa kamar jaririn da aka haifa ba rai ba, kamar jaririn da bai taɓa ganin hasken rana ba.
Or like a miscarriage hidden not was I? like children [who] not they have seen light.
17 A wurin mugaye za su daina yin mugunta, gajiyayyu kuma za su huta.
There wicked [people] they cease turmoil and there they rest weary [ones] of strength.
18 Waɗanda aka daure za su sami jin daɗin; an sake su ba za su sāke jin ana tsawata masu ba.
Together prisoners they are at ease not they hear [the] voice of a taskmaster.
19 Manyan da ƙanana suna a can, bawa kuma ya sami’yanci daga wurin maigidansa.
Small and great [is] there he and a slave [is] free from master his.
20 “Don me ake ba da haske ga waɗanda suke cikin ƙunci, rai kuma ga masu ɗacin rai
Why? does someone give to a sufferer light and life to [people] bitter of soul.
21 ga waɗanda suke neman mutuwa amma ba su samu ba, waɗanda suke nemanta kamar wani abu mai daraja a ɓoye,
Those [who] long for death and there not [is] it and they dug for it more than hidden treasures.
22 waɗanda suke farin ciki sa’ad da suka kai kabari?
The joyful [people] to rejoicing they exult if they find [the] grave.
23 Don me aka ba mutum rai, mutumin da bai san wani abu game da kansa ba, mutumin da Allah ya kange shi.
To a man whom way his it is hidden and he has made inaccessible God behind him.
24 Baƙin ciki ya ishe ni maimakon abinci; ina ta yin nishi ba fasawa;
If before food my groaning my it comes and they poured forth like water cries of distress my.
25 Abin da nake tsoro ya faru da ni; abin da ba na so ya same ni.
For a fear I feared and it came to me and [that] which I dreaded it came to me.
26 Ba ni da salama, ba natsuwa; ba ni da hutu, sai wahala kawai.”
Not I am at ease - and not I am at peace and not I am at rest and it has come turmoil.

< Ayuba 3 >