< Ayuba 3 >

1 Bayan wannan Ayuba ya buɗe baki ya la’anta ranar da aka haife shi.
After this Job opened his mouth, and cursed his day,
2 Ayuba ya ce,
saying,
3 “A hallaka ranar da aka haife ni, da kuma daren da aka ce, ‘An haifi jariri namiji!’
Let the day perish in which I was born, and that night in which they said, Behold a man-child!
4 Bari ranan nan ta zama duhu; kada Allah yă kula da ita; kada rana tă yi haske a wannan rana.
Let that night be darkness, and let not the Lord regard it from above, neither let light come upon it.
5 Bari duhu da inuwa mai duhu ta sāke rufe ta; gizagizai kuma su rufe ta; duhu kuma ya rufe haskenta.
But let darkness and the shadow of death seize it; let blackness come upon it;
6 Bari duhu mai yawa yă rufe daren nan; kada a haɗa ta cikin kwanakin shekara, ko kuma cikin kwanakin watanni.
let that day and night be cursed, let darkness carry them away; let it not come into the days of the year, neither let it be numbered with the days of the months.
7 Bari daren yă zama marar amfani; kada a ji wata sowa ta farin ciki.
But let that night be pain, and let not mirth come upon it, nor joy.
8 Bari waɗanda suke la’anta ranaku su la’anta wannan rana su waɗanda suke umartar dodon ruwa.
But let him that curses that day curse it, [even] he that is ready to attack the great whale.
9 Bari taurarinta na safe su zama duhu; bari ranar tă yi ta jiran ganin haske amma kada tă gani,
Let the stars of that night be darkened; let it remain [dark], and not come into light; and let it not see the morning star arise:
10 gama ba tă hana uwata ɗaukar cikina, don ta hana ni shan wahalan nan ba.
because it shut not up the gates of my mother's womb, for [so] it would have removed sorrow from my eyes.
11 “Me ya sa ban mutu ba da za a haife ni, ko kuma in mutu sa’ad da ana haihuwata ba?
For why died I not in the belly? and [why] did I not come forth from the womb and die immediately?
12 Me ya sa aka haife ni, aka tanada nono na sha na rayu?
and why did the knees support me? and why did I suck the breasts?
13 Da yanzu ina kwance cikin salama; da ina barcina cikin salama
Now I should have lain down and been quiet, I should have slept and been at rest,
14 tare da sarakuna da mashawarta a cikin ƙasa, waɗanda suka gina wa kansu wuraren da yanzu duk sun rushe,
with kings [and] councillors of the earth, who gloried in [their] swords;
15 da shugabanni waɗanda suke da zinariya, waɗanda suka cika gidajensu da azurfa.
or with rulers, whose gold was abundant, who filled their houses with silver:
16 Ko kuma don me ba a ɓoye ni a cikin ƙasa kamar jaririn da aka haifa ba rai ba, kamar jaririn da bai taɓa ganin hasken rana ba.
or [I should have been] as an untimely birth proceeding from his mother's womb, or as infants who never saw light.
17 A wurin mugaye za su daina yin mugunta, gajiyayyu kuma za su huta.
There the ungodly have burnt out the fury of rage; there the wearied in body rest.
18 Waɗanda aka daure za su sami jin daɗin; an sake su ba za su sāke jin ana tsawata masu ba.
And the men of old time have together ceased to hear the exactor's voice.
19 Manyan da ƙanana suna a can, bawa kuma ya sami’yanci daga wurin maigidansa.
The small and great are there, and the servant that feared his lord.
20 “Don me ake ba da haske ga waɗanda suke cikin ƙunci, rai kuma ga masu ɗacin rai
For why is light given to those who are in bitterness, and life to those souls which are in griefs?
21 ga waɗanda suke neman mutuwa amma ba su samu ba, waɗanda suke nemanta kamar wani abu mai daraja a ɓoye,
who desire death, and obtain it not, digging [for it] as [for] treasures;
22 waɗanda suke farin ciki sa’ad da suka kai kabari?
and would be very joyful if they should gain it?
23 Don me aka ba mutum rai, mutumin da bai san wani abu game da kansa ba, mutumin da Allah ya kange shi.
Death [is] rest to [such] a man, for God has hedged him in.
24 Baƙin ciki ya ishe ni maimakon abinci; ina ta yin nishi ba fasawa;
For my groaning comes before my food, and I weep being beset with terror.
25 Abin da nake tsoro ya faru da ni; abin da ba na so ya same ni.
For the terror of which I meditated has come upon me, and that which I had feared has befallen me.
26 Ba ni da salama, ba natsuwa; ba ni da hutu, sai wahala kawai.”
I was not at peace, nor quiet, nor had I rest; yet wrath came upon me.

< Ayuba 3 >