< Ayuba 3 >

1 Bayan wannan Ayuba ya buɗe baki ya la’anta ranar da aka haife shi.
After this, Job opened his mouth and cursed the day of his birth.
2 Ayuba ya ce,
And this is what he said:
3 “A hallaka ranar da aka haife ni, da kuma daren da aka ce, ‘An haifi jariri namiji!’
“May the day of my birth perish, and the night it was said, ‘A boy is conceived.’
4 Bari ranan nan ta zama duhu; kada Allah yă kula da ita; kada rana tă yi haske a wannan rana.
If only that day had turned to darkness! May God above disregard it; may no light shine upon it.
5 Bari duhu da inuwa mai duhu ta sāke rufe ta; gizagizai kuma su rufe ta; duhu kuma ya rufe haskenta.
May darkness and gloom reclaim it, and a cloud settle over it; may the blackness of the day overwhelm it.
6 Bari duhu mai yawa yă rufe daren nan; kada a haɗa ta cikin kwanakin shekara, ko kuma cikin kwanakin watanni.
If only darkness had taken that night away! May it not appear among the days of the year; may it never be entered in any of the months.
7 Bari daren yă zama marar amfani; kada a ji wata sowa ta farin ciki.
Behold, may that night be barren; may no joyful voice come into it.
8 Bari waɗanda suke la’anta ranaku su la’anta wannan rana su waɗanda suke umartar dodon ruwa.
May it be cursed by those who curse the day — those prepared to rouse Leviathan.
9 Bari taurarinta na safe su zama duhu; bari ranar tă yi ta jiran ganin haske amma kada tă gani,
May its morning stars grow dark; may it wait in vain for daylight; may it not see the breaking of dawn.
10 gama ba tă hana uwata ɗaukar cikina, don ta hana ni shan wahalan nan ba.
For that night did not shut the doors of the womb to hide the sorrow from my eyes.
11 “Me ya sa ban mutu ba da za a haife ni, ko kuma in mutu sa’ad da ana haihuwata ba?
Why did I not perish at birth; why did I not die as I came from the womb?
12 Me ya sa aka haife ni, aka tanada nono na sha na rayu?
Why were there knees to receive me, and breasts that I should be nursed?
13 Da yanzu ina kwance cikin salama; da ina barcina cikin salama
For now I would be lying down in peace; I would be asleep and at rest
14 tare da sarakuna da mashawarta a cikin ƙasa, waɗanda suka gina wa kansu wuraren da yanzu duk sun rushe,
with kings and counselors of the earth, who built for themselves cities now in ruins,
15 da shugabanni waɗanda suke da zinariya, waɗanda suka cika gidajensu da azurfa.
or with princes who had gold, who filled their houses with silver.
16 Ko kuma don me ba a ɓoye ni a cikin ƙasa kamar jaririn da aka haifa ba rai ba, kamar jaririn da bai taɓa ganin hasken rana ba.
Or why was I not hidden like a stillborn child, like an infant who never sees daylight?
17 A wurin mugaye za su daina yin mugunta, gajiyayyu kuma za su huta.
There the wicked cease from raging, and there the weary find rest.
18 Waɗanda aka daure za su sami jin daɗin; an sake su ba za su sāke jin ana tsawata masu ba.
The captives enjoy their ease; they do not hear the voice of the oppressor.
19 Manyan da ƙanana suna a can, bawa kuma ya sami’yanci daga wurin maigidansa.
Both small and great are there, and the slave is freed from his master.
20 “Don me ake ba da haske ga waɗanda suke cikin ƙunci, rai kuma ga masu ɗacin rai
Why is light given to the miserable, and life to the bitter of soul,
21 ga waɗanda suke neman mutuwa amma ba su samu ba, waɗanda suke nemanta kamar wani abu mai daraja a ɓoye,
who long for death that does not come, and search for it like hidden treasure,
22 waɗanda suke farin ciki sa’ad da suka kai kabari?
who rejoice and greatly exult when they can find the grave?
23 Don me aka ba mutum rai, mutumin da bai san wani abu game da kansa ba, mutumin da Allah ya kange shi.
Why is life given to a man whose way is hidden, whom God has hedged in?
24 Baƙin ciki ya ishe ni maimakon abinci; ina ta yin nishi ba fasawa;
I sigh when food is put before me, and my groans pour out like water.
25 Abin da nake tsoro ya faru da ni; abin da ba na so ya same ni.
For the thing I feared has overtaken me, and what I dreaded has befallen me.
26 Ba ni da salama, ba natsuwa; ba ni da hutu, sai wahala kawai.”
I am not at ease or quiet; I have no rest, for trouble has come.”

< Ayuba 3 >