< Ayuba 3 >

1 Bayan wannan Ayuba ya buɗe baki ya la’anta ranar da aka haife shi.
Daarna opende Job zijn mond, en vervloekte zijn dag.
2 Ayuba ya ce,
Want Job antwoordde en zeide:
3 “A hallaka ranar da aka haife ni, da kuma daren da aka ce, ‘An haifi jariri namiji!’
De dag verga, waarin ik geboren ben, en de nacht, waarin men zeide: Een knechtje is ontvangen;
4 Bari ranan nan ta zama duhu; kada Allah yă kula da ita; kada rana tă yi haske a wannan rana.
Diezelve dag zij duisternis; dat God naar hem niet vrage van boven; en dat geen glans over hem schijne;
5 Bari duhu da inuwa mai duhu ta sāke rufe ta; gizagizai kuma su rufe ta; duhu kuma ya rufe haskenta.
Dat de duisternis en des doods schaduw hem verontreinigen; dat wolken over hem wonen; dat hem verschrikken de zwarte dampen des dags!
6 Bari duhu mai yawa yă rufe daren nan; kada a haɗa ta cikin kwanakin shekara, ko kuma cikin kwanakin watanni.
Diezelve nacht, donkerheid neme hem in; dat hij zich niet verheuge onder de dagen des jaars; dat hij in het getal der maanden niet kome!
7 Bari daren yă zama marar amfani; kada a ji wata sowa ta farin ciki.
Ziet, diezelve nacht zij eenzaam; dat geen vrolijk gezang daarin kome;
8 Bari waɗanda suke la’anta ranaku su la’anta wannan rana su waɗanda suke umartar dodon ruwa.
Dat hem vervloeken de vervloekers des dags, die bereid zijn hun rouw te verwekken;
9 Bari taurarinta na safe su zama duhu; bari ranar tă yi ta jiran ganin haske amma kada tă gani,
Dat de sterren van zijn schemertijd verduisterd worden; hij wachte naar het licht, en het worde niet; en hij zie niet de oogleden des dageraads!
10 gama ba tă hana uwata ɗaukar cikina, don ta hana ni shan wahalan nan ba.
Omdat hij niet toegesloten heeft de deuren mijns buiks, noch verborgen de moeite van mijn ogen.
11 “Me ya sa ban mutu ba da za a haife ni, ko kuma in mutu sa’ad da ana haihuwata ba?
Waarom ben ik niet gestorven van de baarmoeder af, en heb den geest gegeven, als ik uit den buik voortkwam?
12 Me ya sa aka haife ni, aka tanada nono na sha na rayu?
Waarom zijn mij de knieen voorgekomen, en waartoe de borsten, opdat ik zuigen zou?
13 Da yanzu ina kwance cikin salama; da ina barcina cikin salama
Want nu zou ik nederliggen, en stil zijn; ik zou slapen, dan zou voor mij rust wezen;
14 tare da sarakuna da mashawarta a cikin ƙasa, waɗanda suka gina wa kansu wuraren da yanzu duk sun rushe,
Met de koningen en raadsheren der aarde, die voor zich woeste plaatsen bebouwden;
15 da shugabanni waɗanda suke da zinariya, waɗanda suka cika gidajensu da azurfa.
Of met de vorsten, die goud hadden, die hun huizen met zilver vervulden.
16 Ko kuma don me ba a ɓoye ni a cikin ƙasa kamar jaririn da aka haifa ba rai ba, kamar jaririn da bai taɓa ganin hasken rana ba.
Of als een verborgene misdracht, zou ik niet zijn; als de kinderkens, die het licht niet gezien hebben.
17 A wurin mugaye za su daina yin mugunta, gajiyayyu kuma za su huta.
Daar houden de bozen op van beroering, en daar rusten de vermoeiden van kracht;
18 Waɗanda aka daure za su sami jin daɗin; an sake su ba za su sāke jin ana tsawata masu ba.
Daar zijn de gebondenen te zamen in rust; zij horen de stem des drijvers niet.
19 Manyan da ƙanana suna a can, bawa kuma ya sami’yanci daga wurin maigidansa.
De kleine en de grote is daar; en de knecht vrij van zijn heer.
20 “Don me ake ba da haske ga waɗanda suke cikin ƙunci, rai kuma ga masu ɗacin rai
Waarom geeft Hij den ellendigen het licht, en het leven den bitterlijk bedroefden van gemoed?
21 ga waɗanda suke neman mutuwa amma ba su samu ba, waɗanda suke nemanta kamar wani abu mai daraja a ɓoye,
Die verlangen naar den dood, maar hij is er niet; en graven daarnaar meer dan naar verborgene schatten;
22 waɗanda suke farin ciki sa’ad da suka kai kabari?
Die blijde zijn tot opspringens toe, en zich verheugen, als zij het graf vinden;
23 Don me aka ba mutum rai, mutumin da bai san wani abu game da kansa ba, mutumin da Allah ya kange shi.
Aan den man, wiens weg verborgen is, en dien God overdekt heeft?
24 Baƙin ciki ya ishe ni maimakon abinci; ina ta yin nishi ba fasawa;
Want voor mijn brood komt mijn zuchting; en mijn brullingen worden uitgestort als water.
25 Abin da nake tsoro ya faru da ni; abin da ba na so ya same ni.
Want ik vreesde een vreze, en zij is mij aangekomen; en wat ik schroomde, is mij overkomen.
26 Ba ni da salama, ba natsuwa; ba ni da hutu, sai wahala kawai.”
Ik was niet gerust; en was niet stil, en rustte niet; en de beroering is gekomen.

< Ayuba 3 >