< Ayuba 3 >
1 Bayan wannan Ayuba ya buɗe baki ya la’anta ranar da aka haife shi.
Derefter oplod Job sin Mund og forbandede sin Dag,
og Job tog til Orde og sagde:
3 “A hallaka ranar da aka haife ni, da kuma daren da aka ce, ‘An haifi jariri namiji!’
Bort med den Dag, jeg fødtes, den Nat, der sagde: "Se, en Dreng!"
4 Bari ranan nan ta zama duhu; kada Allah yă kula da ita; kada rana tă yi haske a wannan rana.
Denne Dag vorde Mørke, Gud deroppe spørge ej om den, over den stråle ej Lyset frem!
5 Bari duhu da inuwa mai duhu ta sāke rufe ta; gizagizai kuma su rufe ta; duhu kuma ya rufe haskenta.
Mulm og Mørke løse den ind, Tåge lægge sig over den, Formørkelser skræmme den!
6 Bari duhu mai yawa yă rufe daren nan; kada a haɗa ta cikin kwanakin shekara, ko kuma cikin kwanakin watanni.
Mørket tage den Nat, den høre ej hjemme blandt Årets Dage, den komme ikke i Måneders Tal!
7 Bari daren yă zama marar amfani; kada a ji wata sowa ta farin ciki.
Ja, denne Nat vorde gold, der lyde ej Jubel i den!
8 Bari waɗanda suke la’anta ranaku su la’anta wannan rana su waɗanda suke umartar dodon ruwa.
De, der besværger Dage, forbande den, de, der har lært at hidse Livjatan";
9 Bari taurarinta na safe su zama duhu; bari ranar tă yi ta jiran ganin haske amma kada tă gani,
dens Morgenstjerner formørkes, den bie forgæves på Lys, den skue ej Morgenrødens Øjenlåg,
10 gama ba tă hana uwata ɗaukar cikina, don ta hana ni shan wahalan nan ba.
fordi den ej lukked mig Moderlivets Døre og skjulte Kvide for mit Blik!
11 “Me ya sa ban mutu ba da za a haife ni, ko kuma in mutu sa’ad da ana haihuwata ba?
Hvi døde jeg ikke i Moders Liv eller udånded straks fra Moders Skød?
12 Me ya sa aka haife ni, aka tanada nono na sha na rayu?
Hvorfor var der Knæ til at tage imod mig, hvorfor var der Bryster at die?
13 Da yanzu ina kwance cikin salama; da ina barcina cikin salama
Så havde jeg nu ligget og hvilet, så havde jeg slumret i Fred
14 tare da sarakuna da mashawarta a cikin ƙasa, waɗanda suka gina wa kansu wuraren da yanzu duk sun rushe,
blandt Konger og Jordens Styrere, der bygged sig Gravpaladser,
15 da shugabanni waɗanda suke da zinariya, waɗanda suka cika gidajensu da azurfa.
blandt Fyrster, rige på Guld, som fyldte deres Huse med Sølv.
16 Ko kuma don me ba a ɓoye ni a cikin ƙasa kamar jaririn da aka haifa ba rai ba, kamar jaririn da bai taɓa ganin hasken rana ba.
Eller var jeg dog som et nedgravet Foster. som Børn, der ikke fik Lyset at se!
17 A wurin mugaye za su daina yin mugunta, gajiyayyu kuma za su huta.
Der larmer de gudløse ikke mer, der hviler de trætte ud,
18 Waɗanda aka daure za su sami jin daɗin; an sake su ba za su sāke jin ana tsawata masu ba.
alle de fangne har Ro, de hører ej Fogedens Røst;
19 Manyan da ƙanana suna a can, bawa kuma ya sami’yanci daga wurin maigidansa.
små og store er lige der og Trællen fri for sin Herre.
20 “Don me ake ba da haske ga waɗanda suke cikin ƙunci, rai kuma ga masu ɗacin rai
Hvi giver Gud de lidende Lys, de bittert sørgende Liv,
21 ga waɗanda suke neman mutuwa amma ba su samu ba, waɗanda suke nemanta kamar wani abu mai daraja a ɓoye,
dem, som bier forgæves på Døden, graver derefter som efter Skatte,
22 waɗanda suke farin ciki sa’ad da suka kai kabari?
som glæder sig til en Stenhøj, jubler, når de finder deres Grav
23 Don me aka ba mutum rai, mutumin da bai san wani abu game da kansa ba, mutumin da Allah ya kange shi.
en Mand, hvis Vej er skjult, hvem Gud har stænget inde?
24 Baƙin ciki ya ishe ni maimakon abinci; ina ta yin nishi ba fasawa;
Thi Suk er blevet mit daglige Brød, mine Ve råb strømmer som Vand.
25 Abin da nake tsoro ya faru da ni; abin da ba na so ya same ni.
Thi hvad jeg gruer for, rammer mig, hvad jeg bæver for, kommer over mig.
26 Ba ni da salama, ba natsuwa; ba ni da hutu, sai wahala kawai.”
Knap har jeg Fred, og knap har jeg Ro, knap har jeg Hvile, så kommer Uro!