< Ayuba 29 >

1 Ayuba ya ci gaba da jawabinsa,
Job siguió hablando.
2 “Da ma ina nan lokacin da ya wuce baya can, kwanakin da Allah yake lura da ni,
“¡Ojalá volviera a los viejos tiempos en que Dios me cuidaba!
3 lokacin da fitilarsa take haske a kaina na yi tafiya cikin duhu tare da haskensa.
Su luz brillaba sobre mí y alumbraba mi camino en la oscuridad.
4 Kwanakin da nake tasowa, lokacin da abokantakar Allah ta sa wa gidana albarka,
Cuando era joven y fuerte, Dios era mi amigo y me hablaba en mi casa.
5 lokacin da Maɗaukaki yana tare da ni, kuma’ya’yana suna kewaye da ni,
El Todopoderoso seguía conmigo y estaba rodeado de mis hijos.
6 lokacin da ake zuba madara a inda nake takawa, duwatsu kuma suna ɓulɓulo mini man zaitun.
Mis rebaños producían mucha leche, y el aceite fluía libremente de mis prensas de aceitunas.
7 “Sa’ad da na je ƙofar birni na zauna a bainin jama’a,
Salí a la puerta de la ciudad y me senté en la plaza pública.
8 matasan da suka gan ni sukan ja gefe tsofaffi kuma suka tashi tsaye;
Los jóvenes me veían y se apartaban del camino; los ancianos me defendían.
9 sarakuna suka yi shiru suka rufe bakunansu da hannuwansu;
Los dirigentes guardaron silencio y se taparon la boca con las manos.
10 Muryar manya ta yi tsit harshensu ya manne a rufin bakunansu.
Las voces de los funcionarios se acallaron; se callaron en mi presencia.
11 Duk wanda ya ji ni ya yaba mini waɗanda suka gan ni kuma sun amince da ni,
“Todos los que me escuchaban me alababan; los que me veían me elogiaban,
12 domin na ceci matalauta waɗanda suka nemi taimako, da marasa mahaifi waɗanda ba su da wanda zai taimake su.
porque daba a los pobres que me llamaban y a los huérfanos que no tenían quien los ayudara.
13 Mutumin da yake bakin mutuwa ya sa mini albarka. Na faranta wa gwauruwa zuciya.
Los que estaban a punto de morir me bendijeron; hice cantar de alegría a la viuda.
14 Na yafa adalci ya zama suturata; gaskiya ita ce rigata da rawanina.
Siendo sincero y actuando correctamente eran lo que yo llevaba como ropa.
15 Ni ne idon makafi kuma ƙafa ga guragu.
Fui como los ojos para los ciegos y los pies para los cojos.
16 Ni mahaifi ne ga masu bukata; na tsaya wa baƙo.
Fui como un padre para los pobres, y defendí los derechos de los extranjeros.
17 Na karya ƙarfin mugaye na ƙwato waɗanda suke riƙe da haƙoransu.
Rompí la mandíbula de los malvados y les hice soltar su presa de los dientes.
18 “Na yi tunani cewa, ‘Zan mutu a cikin gidana, kwanakina da yawa kamar turɓayar ƙasa.
Pensé que moriría en casa, después de muchos años.
19 Jijiyoyina za su kai cikin ruwa, kuma raɓa za tă kwanta a rassana dukan dare.
Como un árbol, mis raíces se extienden hasta el agua; el rocío se posa en mis ramas durante la noche.
20 Ɗaukakata za tă kasance tare da ni garau, bakana koyaushe sabo ne a hannuna.’
Siempre se me concedían nuevos honores; mi fuerza se renovaba como un arco infalible.
21 “Mutane suna mai da hankali su saurare ni, suna yin shiru don su ji shawarata.
“La gente escuchaba atentamente lo que yo decía; se callaba al escuchar mis consejos.
22 Bayan da na yi magana, ba su ƙara ce kome ba. Maganata ta shige su.
Una vez que yo hablaba, no tenían nada más que decir; lo que yo decía era suficiente.
23 Sukan jira ni kamar yadda ake jiran ruwan sama. Sukan sha daga cikin maganganuna kamar mai shan ruwan bazara.
Me esperaban como quien espera la lluvia, con la boca abierta por la lluvia de primavera.
24 Sa’ad da na yi musu murmushi da ƙyar sukan yarda; hasken fuskata yana da daraja a gare su.
Cuando les sonreía, apenas podían creerlo; mi aprobación significaba todo el mundo para ellos.
25 Na zaɓar masu inda za su bi na kuma zauna kamar sarkinsu; na zauna kamar sarki a cikin rundunansu; ina nan kamar mai yi wa masu makoki ta’aziyya.
Decidí el camino a seguir como su líder, viviendo como un rey entre sus soldados, y cuando estaban tristes los consolaba”.

< Ayuba 29 >