< Ayuba 29 >

1 Ayuba ya ci gaba da jawabinsa,
E proseguiu Job em proferir o seu dito, e disse:
2 “Da ma ina nan lokacin da ya wuce baya can, kwanakin da Allah yake lura da ni,
Ah! quem me dera ser como eu fui nos meses passados! como nos dias em que Deus me guardava!
3 lokacin da fitilarsa take haske a kaina na yi tafiya cikin duhu tare da haskensa.
Quando fazia resplandecer a sua candeia sobre a minha cabeça e quando eu pela sua luz caminhava pelas trevas:
4 Kwanakin da nake tasowa, lokacin da abokantakar Allah ta sa wa gidana albarka,
Como era nos dias da minha mocidade, quando o segredo de Deus estava sobre a minha tenda:
5 lokacin da Maɗaukaki yana tare da ni, kuma’ya’yana suna kewaye da ni,
Quando o Todo-poderoso ainda estava comigo, e os meus meninos em redor de mim.
6 lokacin da ake zuba madara a inda nake takawa, duwatsu kuma suna ɓulɓulo mini man zaitun.
Quando lavava os meus passos na manteiga, e da rocha me corriam ribeiros de azeite:
7 “Sa’ad da na je ƙofar birni na zauna a bainin jama’a,
Quando saía a porta pela cidade, e na praça fazia preparar a minha cadeira:
8 matasan da suka gan ni sukan ja gefe tsofaffi kuma suka tashi tsaye;
Os moços me viam, e se escondiam, e até os idosos se levantavam e se punham em pé:
9 sarakuna suka yi shiru suka rufe bakunansu da hannuwansu;
Os príncipes continham as suas palavras, e punham a mão sobre a sua boca:
10 Muryar manya ta yi tsit harshensu ya manne a rufin bakunansu.
A voz dos chefes se escondia: e a sua língua se pegava ao seu paladar:
11 Duk wanda ya ji ni ya yaba mini waɗanda suka gan ni kuma sun amince da ni,
Ouvindo-me algum ouvido, me tinha por bem-aventurado: vendo-me algum olho, dava testemunho de mim;
12 domin na ceci matalauta waɗanda suka nemi taimako, da marasa mahaifi waɗanda ba su da wanda zai taimake su.
Porque eu livrava o miserável, que clamava: como também o órfão que não tinha quem o socoresse.
13 Mutumin da yake bakin mutuwa ya sa mini albarka. Na faranta wa gwauruwa zuciya.
A benção do que ia perecendo vinha sobre mim, e eu fazia que jubilasse o coração da viúva.
14 Na yafa adalci ya zama suturata; gaskiya ita ce rigata da rawanina.
Vestia-me da justiça: e ela me servia de vestido: como manto e diadema era o meu juízo.
15 Ni ne idon makafi kuma ƙafa ga guragu.
Eu fui o olho do cego, como também os pés do coxo:
16 Ni mahaifi ne ga masu bukata; na tsaya wa baƙo.
Aos necessitados era pai, e as causas de que eu não tinha conhecimento inquiria com diligência;
17 Na karya ƙarfin mugaye na ƙwato waɗanda suke riƙe da haƙoransu.
E quebrava os queixais do perverso, e dos seus dentes tirava a preza.
18 “Na yi tunani cewa, ‘Zan mutu a cikin gidana, kwanakina da yawa kamar turɓayar ƙasa.
E dizia: No meu ninho expirarei, e multiplicarei os meus dias como a areia.
19 Jijiyoyina za su kai cikin ruwa, kuma raɓa za tă kwanta a rassana dukan dare.
A minha raiz se estendia junto às águas, e o orvalho fazia assento sobre os meus ramos;
20 Ɗaukakata za tă kasance tare da ni garau, bakana koyaushe sabo ne a hannuna.’
A minha honra se renovava em mim, e o meu arco se reforçava na minha mão.
21 “Mutane suna mai da hankali su saurare ni, suna yin shiru don su ji shawarata.
Ouvindo-me esperavam, e em silêncio atendiam ao meu conselho.
22 Bayan da na yi magana, ba su ƙara ce kome ba. Maganata ta shige su.
Acabada a minha palavra, não replicavam, e minhas razões destilavam sobre eles;
23 Sukan jira ni kamar yadda ake jiran ruwan sama. Sukan sha daga cikin maganganuna kamar mai shan ruwan bazara.
Porque me esperavam, como a chuva; e abriam a sua boca, como a chuva tardia
24 Sa’ad da na yi musu murmushi da ƙyar sukan yarda; hasken fuskata yana da daraja a gare su.
Se me ria para eles, não o criam, e não faziam abater a luz do meu rosto;
25 Na zaɓar masu inda za su bi na kuma zauna kamar sarkinsu; na zauna kamar sarki a cikin rundunansu; ina nan kamar mai yi wa masu makoki ta’aziyya.
Eu escolhia o seu caminho, assentava-me como chefe, e habitava como rei entre as tropas: como aquele que consola os que pranteiam.

< Ayuba 29 >