< Ayuba 29 >

1 Ayuba ya ci gaba da jawabinsa,
Giobbe continuò a pronunziare le sue sentenze e disse:
2 “Da ma ina nan lokacin da ya wuce baya can, kwanakin da Allah yake lura da ni,
Oh, potessi tornare com'ero ai mesi di un tempo, ai giorni in cui Dio mi proteggeva,
3 lokacin da fitilarsa take haske a kaina na yi tafiya cikin duhu tare da haskensa.
quando brillava la sua lucerna sopra il mio capo e alla sua luce camminavo in mezzo alle tenebre;
4 Kwanakin da nake tasowa, lokacin da abokantakar Allah ta sa wa gidana albarka,
com'ero ai giorni del mio autunno, quando Dio proteggeva la mia tenda,
5 lokacin da Maɗaukaki yana tare da ni, kuma’ya’yana suna kewaye da ni,
quando l'Onnipotente era ancora con me e i giovani mi stavano attorno;
6 lokacin da ake zuba madara a inda nake takawa, duwatsu kuma suna ɓulɓulo mini man zaitun.
quando mi lavavo in piedi nel latte e la roccia mi versava ruscelli d'olio!
7 “Sa’ad da na je ƙofar birni na zauna a bainin jama’a,
Quando uscivo verso la porta della città e sulla piazza ponevo il mio seggio:
8 matasan da suka gan ni sukan ja gefe tsofaffi kuma suka tashi tsaye;
vedendomi, i giovani si ritiravano e i vecchi si alzavano in piedi;
9 sarakuna suka yi shiru suka rufe bakunansu da hannuwansu;
i notabili sospendevano i discorsi e si mettevan la mano sulla bocca;
10 Muryar manya ta yi tsit harshensu ya manne a rufin bakunansu.
la voce dei capi si smorzava e la loro lingua restava fissa al palato;
11 Duk wanda ya ji ni ya yaba mini waɗanda suka gan ni kuma sun amince da ni,
con gli orecchi ascoltavano e mi dicevano felice, con gli occhi vedevano e mi rendevano testimonianza,
12 domin na ceci matalauta waɗanda suka nemi taimako, da marasa mahaifi waɗanda ba su da wanda zai taimake su.
perché soccorrevo il povero che chiedeva aiuto, l'orfano che ne era privo.
13 Mutumin da yake bakin mutuwa ya sa mini albarka. Na faranta wa gwauruwa zuciya.
La benedizione del morente scendeva su di me e al cuore della vedova infondevo la gioia.
14 Na yafa adalci ya zama suturata; gaskiya ita ce rigata da rawanina.
Mi ero rivestito di giustizia come di un vestimento; come mantello e turbante era la mia equità.
15 Ni ne idon makafi kuma ƙafa ga guragu.
Io ero gli occhi per il cieco, ero i piedi per lo zoppo.
16 Ni mahaifi ne ga masu bukata; na tsaya wa baƙo.
Padre io ero per i poveri ed esaminavo la causa dello sconosciuto;
17 Na karya ƙarfin mugaye na ƙwato waɗanda suke riƙe da haƙoransu.
rompevo la mascella al perverso e dai suoi denti strappavo la preda.
18 “Na yi tunani cewa, ‘Zan mutu a cikin gidana, kwanakina da yawa kamar turɓayar ƙasa.
Pensavo: «Spirerò nel mio nido e moltiplicherò come sabbia i miei giorni».
19 Jijiyoyina za su kai cikin ruwa, kuma raɓa za tă kwanta a rassana dukan dare.
La mia radice avrà adito alle acque e la rugiada cadrà di notte sul mio ramo.
20 Ɗaukakata za tă kasance tare da ni garau, bakana koyaushe sabo ne a hannuna.’
La mia gloria sarà sempre nuova e il mio arco si rinforzerà nella mia mano.
21 “Mutane suna mai da hankali su saurare ni, suna yin shiru don su ji shawarata.
Mi ascoltavano in attesa fiduciosa e tacevano per udire il mio consiglio.
22 Bayan da na yi magana, ba su ƙara ce kome ba. Maganata ta shige su.
Dopo le mie parole non replicavano e su di loro scendevano goccia a goccia i miei detti.
23 Sukan jira ni kamar yadda ake jiran ruwan sama. Sukan sha daga cikin maganganuna kamar mai shan ruwan bazara.
Mi attendevano come si attende la pioggia e aprivano la bocca come ad acqua primaverile.
24 Sa’ad da na yi musu murmushi da ƙyar sukan yarda; hasken fuskata yana da daraja a gare su.
Se a loro sorridevo, non osavano crederlo, né turbavano la serenità del mio volto.
25 Na zaɓar masu inda za su bi na kuma zauna kamar sarkinsu; na zauna kamar sarki a cikin rundunansu; ina nan kamar mai yi wa masu makoki ta’aziyya.
Indicavo loro la via da seguire e sedevo come capo, e vi rimanevo come un re fra i soldati o come un consolatore d'afflitti.

< Ayuba 29 >