< Ayuba 29 >
1 Ayuba ya ci gaba da jawabinsa,
Darauf fuhr Job im Vortrag seiner Rede fort:
2 “Da ma ina nan lokacin da ya wuce baya can, kwanakin da Allah yake lura da ni,
"Ach, daß ich wäre wie in früheren Monden, wie in den Tagen, da mich Gott beschützte,
3 lokacin da fitilarsa take haske a kaina na yi tafiya cikin duhu tare da haskensa.
als seine Leuchte über meinem Haupte schwebte und ich bei ihrem Scheine mich ins Dunkel wagte!
4 Kwanakin da nake tasowa, lokacin da abokantakar Allah ta sa wa gidana albarka,
So, wie ich war, in meiner höchsten Blüte Tagen, da Gott mein Zelt beschirmte,
5 lokacin da Maɗaukaki yana tare da ni, kuma’ya’yana suna kewaye da ni,
als der Allmächtige noch mit mir war, als meine Dienerschaft mich noch umgab,
6 lokacin da ake zuba madara a inda nake takawa, duwatsu kuma suna ɓulɓulo mini man zaitun.
als meine Gäste sich in Dickmilch badeten, als Bäche Öls bei mir den Boten zur Verfügung standen!
7 “Sa’ad da na je ƙofar birni na zauna a bainin jama’a,
Wenn ich zur Stadt hinauf zum Tore ging und auf dem Markte meinen Sitz einnahm,
8 matasan da suka gan ni sukan ja gefe tsofaffi kuma suka tashi tsaye;
alsdann verkrochen sich die Knaben, sahn sie mich, und Greise standen auf und blieben stehen.
9 sarakuna suka yi shiru suka rufe bakunansu da hannuwansu;
Die Ratsherrn hielten ein mit Reden und legten auf den Mund die Hand.
10 Muryar manya ta yi tsit harshensu ya manne a rufin bakunansu.
Der Edlen Stimme, sie verbarg sich; das Wort blieb ihnen in der Kehle stecken.
11 Duk wanda ya ji ni ya yaba mini waɗanda suka gan ni kuma sun amince da ni,
Wer von mir hörte, pries mich selig; wer mich erblickte, lobte mich.
12 domin na ceci matalauta waɗanda suka nemi taimako, da marasa mahaifi waɗanda ba su da wanda zai taimake su.
Ich half dem Armen, der um Hilfe schrie, dem Waisenkinde, dem hilflosen.
13 Mutumin da yake bakin mutuwa ya sa mini albarka. Na faranta wa gwauruwa zuciya.
Und armer Menschen Segen kam auf mich; das Herz der Witwe ließ ich jubeln.
14 Na yafa adalci ya zama suturata; gaskiya ita ce rigata da rawanina.
Gerechtigkeit war mein Gewand, das gut mir stand, und meine Rechtlichkeit war Mantel mir und Diadem.
15 Ni ne idon makafi kuma ƙafa ga guragu.
Ich war des Blinden Augenlicht und Fuß dem Lahmen.
16 Ni mahaifi ne ga masu bukata; na tsaya wa baƙo.
Den Armen wollte ich ein Vater sein; selbst Fremder Sache führte ich.
17 Na karya ƙarfin mugaye na ƙwato waɗanda suke riƙe da haƙoransu.
Des Bösewichts Gebiß zermalmte ich und riß den Raub ihm aus den Zähnen.
18 “Na yi tunani cewa, ‘Zan mutu a cikin gidana, kwanakina da yawa kamar turɓayar ƙasa.
So dachte ich, in meinem Neste stürbe ich; ich lebte soviel Jahre wie der Phönix.
19 Jijiyoyina za su kai cikin ruwa, kuma raɓa za tă kwanta a rassana dukan dare.
Zum Wasser reichte meine Wurzel tief hinab; in meinen Zweigen nächtigte der Tau,
20 Ɗaukakata za tă kasance tare da ni garau, bakana koyaushe sabo ne a hannuna.’
und neu stets würde meine Herrlichkeit an mir; in meiner Hand verjüngte sich der Bogen.
21 “Mutane suna mai da hankali su saurare ni, suna yin shiru don su ji shawarata.
Mir hörten sie nur zu und warteten und lauschten schweigend meinem Rat.
22 Bayan da na yi magana, ba su ƙara ce kome ba. Maganata ta shige su.
Wenn ich geredet, sprachen sie nicht mehr; nur meine Rede troff auf sie herab.
23 Sukan jira ni kamar yadda ake jiran ruwan sama. Sukan sha daga cikin maganganuna kamar mai shan ruwan bazara.
Sie warteten auf mich wie auf den Regen; sie lechzten nach mir wie auf Lenzesregen.
24 Sa’ad da na yi musu murmushi da ƙyar sukan yarda; hasken fuskata yana da daraja a gare su.
Und lächelte ich ihnen zu, so konnten sie's nicht glauben, und sie verschmähten nicht mein heitres Antlitz.
25 Na zaɓar masu inda za su bi na kuma zauna kamar sarkinsu; na zauna kamar sarki a cikin rundunansu; ina nan kamar mai yi wa masu makoki ta’aziyya.
Ich wählte ihren Weg, den sie einschlagen sollten, wie bei der Kriegerschar der König. Ich saß gemächlich obenan wie einer, der den Trauernden Trost spendet." -