< Ayuba 29 >
1 Ayuba ya ci gaba da jawabinsa,
Job prenant encore de nouveau sa parabole, dit:
2 “Da ma ina nan lokacin da ya wuce baya can, kwanakin da Allah yake lura da ni,
Qui m’accordera que je sois comme dans les anciens mois, comme aux jours dans lesquels Dieu me gardait;
3 lokacin da fitilarsa take haske a kaina na yi tafiya cikin duhu tare da haskensa.
Quand sa lampe luisait sur ma tête, et qu’à sa lumière je marchais dans les ténèbres;
4 Kwanakin da nake tasowa, lokacin da abokantakar Allah ta sa wa gidana albarka,
Comme je fus aux jours de ma jeunesse, quand en secret Dieu était dans mon tabernacle;
5 lokacin da Maɗaukaki yana tare da ni, kuma’ya’yana suna kewaye da ni,
Quand le Tout-Puissant était avec moi, et qu’autour de moi étaient mes serviteurs;
6 lokacin da ake zuba madara a inda nake takawa, duwatsu kuma suna ɓulɓulo mini man zaitun.
Quand je lavais mes pieds dans le beurre, et qu’une pierre répandait pour moi des ruisseaux d’huile;
7 “Sa’ad da na je ƙofar birni na zauna a bainin jama’a,
Quand je m’avançais vers la porte de la ville, et que sur la place publique on me préparait un siège?
8 matasan da suka gan ni sukan ja gefe tsofaffi kuma suka tashi tsaye;
Les jeunes hommes me voyaient, et se retiraient à l’écart; et les vieillards, se levant, se tenaient debout.
9 sarakuna suka yi shiru suka rufe bakunansu da hannuwansu;
Les princes cessaient de parler, et mettaient un doigt sur leur bouche.
10 Muryar manya ta yi tsit harshensu ya manne a rufin bakunansu.
Les grands retenaient leur voix, et leur langue s’attachait à leur palais.
11 Duk wanda ya ji ni ya yaba mini waɗanda suka gan ni kuma sun amince da ni,
L’oreille qui m’entendait me proclamait bienheureux, et l’œil qui me voyait me rendait témoignage;
12 domin na ceci matalauta waɗanda suka nemi taimako, da marasa mahaifi waɗanda ba su da wanda zai taimake su.
Parce que j’avais délivré le pauvre qui criait, et l’orphelin qui n’avait pas de soutien.
13 Mutumin da yake bakin mutuwa ya sa mini albarka. Na faranta wa gwauruwa zuciya.
La bénédiction de celui qui allait périr venait sur moi, et je consolais le cœur de la veuve.
14 Na yafa adalci ya zama suturata; gaskiya ita ce rigata da rawanina.
Je me suis revêtu de la justice, et l’équité de mes jugements m’a servi comme de vêtement et de diadème.
15 Ni ne idon makafi kuma ƙafa ga guragu.
J’ai été un œil pour l’aveugle, et un pied pour le boiteux.
16 Ni mahaifi ne ga masu bukata; na tsaya wa baƙo.
J’étais le père des pauvres; et l’affaire que je ne connaissais pas, je l’étudiais avec le plus grand soin.
17 Na karya ƙarfin mugaye na ƙwato waɗanda suke riƙe da haƙoransu.
Je brisais les mâchoires de l’injuste, et j’arrachais la proie de ses dents.
18 “Na yi tunani cewa, ‘Zan mutu a cikin gidana, kwanakina da yawa kamar turɓayar ƙasa.
Et je disais: C’est dans mon petit nid que je mourrai, et comme le palmier, je multiplierai mes jours.
19 Jijiyoyina za su kai cikin ruwa, kuma raɓa za tă kwanta a rassana dukan dare.
Ma racine s’étend le long des eaux, et la rosée se reposera sur ma moisson.
20 Ɗaukakata za tă kasance tare da ni garau, bakana koyaushe sabo ne a hannuna.’
Ma gloire se renouvellera tous les jours et mon arc se fortifiera dans ma main.
21 “Mutane suna mai da hankali su saurare ni, suna yin shiru don su ji shawarata.
Ceux qui m’écoutaient attendaient mon sentiment, et, attentifs, ils se tenaient en silence pour recevoir mon avis.
22 Bayan da na yi magana, ba su ƙara ce kome ba. Maganata ta shige su.
Ils n’osaient rien ajouter à mes paroles, et mon discours coulait sur eux goutte à goutte.
23 Sukan jira ni kamar yadda ake jiran ruwan sama. Sukan sha daga cikin maganganuna kamar mai shan ruwan bazara.
Ils me souhaitaient comme l’eau du ciel, et ils ouvraient leur bouche, comme la terre s’ouvre à la pluie de l’arrière-saison.
24 Sa’ad da na yi musu murmushi da ƙyar sukan yarda; hasken fuskata yana da daraja a gare su.
Si quelquefois je leur souriais, ils ne le croyaient pas, et la lumière de mon visage ne tombait pas à terre.
25 Na zaɓar masu inda za su bi na kuma zauna kamar sarkinsu; na zauna kamar sarki a cikin rundunansu; ina nan kamar mai yi wa masu makoki ta’aziyya.
Si je voulais aller parmi eux, j’avais la première place; et lorsque j’étais assis comme un roi entouré de son armée, j’étais cependant le consolateur des affligés.