< Ayuba 29 >

1 Ayuba ya ci gaba da jawabinsa,
Et Job continuant, reprit son discours sentencieux, et dit:
2 “Da ma ina nan lokacin da ya wuce baya can, kwanakin da Allah yake lura da ni,
Oh! qui me ferait être comme j'étais autrefois, comme j'étais en ces jours où Dieu me gardait.
3 lokacin da fitilarsa take haske a kaina na yi tafiya cikin duhu tare da haskensa.
Quand il faisait luire sa lampe sur ma tête, et quand je marchais parmi les ténèbres, [éclairé] par sa lumière.
4 Kwanakin da nake tasowa, lokacin da abokantakar Allah ta sa wa gidana albarka,
Comme j'étais aux jours de mon automne, lorsque le secret de Dieu était dans ma tente.
5 lokacin da Maɗaukaki yana tare da ni, kuma’ya’yana suna kewaye da ni,
Quand le Tout-puissant était encore avec moi, et mes gens autour de moi.
6 lokacin da ake zuba madara a inda nake takawa, duwatsu kuma suna ɓulɓulo mini man zaitun.
Quand je lavais mes pas dans le beurre, et que des ruisseaux d'huile découlaient pour moi du rocher.
7 “Sa’ad da na je ƙofar birni na zauna a bainin jama’a,
Quand je sortais vers la porte passant par la ville, et que je me faisais préparer un siège dans la place,
8 matasan da suka gan ni sukan ja gefe tsofaffi kuma suka tashi tsaye;
Les jeunes gens me voyant se cachaient, les vieillards se levaient, et se tenaient debout.
9 sarakuna suka yi shiru suka rufe bakunansu da hannuwansu;
Les principaux s'abstenaient de parler, et mettaient la main sur leur bouche.
10 Muryar manya ta yi tsit harshensu ya manne a rufin bakunansu.
Les Conducteurs retenaient leur voix, et leur langue était attachée à leur palais.
11 Duk wanda ya ji ni ya yaba mini waɗanda suka gan ni kuma sun amince da ni,
L'oreille qui m'entendait, disait que j'étais bienheureux, et l'œil qui me voyait, déposait en ma faveur.
12 domin na ceci matalauta waɗanda suka nemi taimako, da marasa mahaifi waɗanda ba su da wanda zai taimake su.
Car je délivrais l'affligé qui criait, et l'orphelin qui n'avait personne pour le secourir.
13 Mutumin da yake bakin mutuwa ya sa mini albarka. Na faranta wa gwauruwa zuciya.
La bénédiction de celui qui s'en allait périr, venait sur moi, et je faisais que le cœur de la veuve chantait de joie.
14 Na yafa adalci ya zama suturata; gaskiya ita ce rigata da rawanina.
J'étais revêtu de la justice, elle me servait de vêtement, et mon équité m'était comme un manteau, et [comme] une tiare.
15 Ni ne idon makafi kuma ƙafa ga guragu.
Je servais d'œil à l'aveugle, et de pieds au boiteux.
16 Ni mahaifi ne ga masu bukata; na tsaya wa baƙo.
J'étais le père des pauvres, et je m'informais diligemment de la cause qui ne m'était point connue.
17 Na karya ƙarfin mugaye na ƙwato waɗanda suke riƙe da haƙoransu.
Je cassais les grosses dents de l'injuste, et je lui arrachais la proie d'entre ses dents.
18 “Na yi tunani cewa, ‘Zan mutu a cikin gidana, kwanakina da yawa kamar turɓayar ƙasa.
C'est pourquoi je disais: Je mourrai dans mon lit, et je multiplierai mes jours comme les grains de sable.
19 Jijiyoyina za su kai cikin ruwa, kuma raɓa za tă kwanta a rassana dukan dare.
Ma racine était ouverte aux eaux, et la rosée demeurait toute la nuit sur mes branches.
20 Ɗaukakata za tă kasance tare da ni garau, bakana koyaushe sabo ne a hannuna.’
Ma gloire se renouvelait en moi, et mon arc était renforcé en ma main.
21 “Mutane suna mai da hankali su saurare ni, suna yin shiru don su ji shawarata.
On m'écoutait, et on attendait [que j'eusse parlé]; et lorsque j'avais dit mon avis, on se tenait dans le silence.
22 Bayan da na yi magana, ba su ƙara ce kome ba. Maganata ta shige su.
Ils ne répliquaient rien après ce que je disais, et ma parole se répandait sur eux [comme une rosée].
23 Sukan jira ni kamar yadda ake jiran ruwan sama. Sukan sha daga cikin maganganuna kamar mai shan ruwan bazara.
Ils m'attendaient comme on attend la pluie; ils ouvraient leur bouche, comme après la pluie de la dernière saison.
24 Sa’ad da na yi musu murmushi da ƙyar sukan yarda; hasken fuskata yana da daraja a gare su.
Riais-je avec eux? ils ne le croyaient point; et ils ne faisaient point disparaître la sérénité de mon visage.
25 Na zaɓar masu inda za su bi na kuma zauna kamar sarkinsu; na zauna kamar sarki a cikin rundunansu; ina nan kamar mai yi wa masu makoki ta’aziyya.
Voulais-je aller avec eux? j'étais assis au haut bout, j'étais entr'eux comme un Roi dans son armée, et comme un homme qui console les affligés.

< Ayuba 29 >