< Ayuba 29 >
1 Ayuba ya ci gaba da jawabinsa,
Job reprit encore son discours et dit:
2 “Da ma ina nan lokacin da ya wuce baya can, kwanakin da Allah yake lura da ni,
Oh! Qui me rendra les mois d’autrefois, les jours où Dieu veillait à ma garde;
3 lokacin da fitilarsa take haske a kaina na yi tafiya cikin duhu tare da haskensa.
quand sa lampe brillait sur ma tête, et que sa lumière me guidait dans les ténèbres!
4 Kwanakin da nake tasowa, lokacin da abokantakar Allah ta sa wa gidana albarka,
Tel que j’étais aux jours de mon âge mûr, quand Dieu me visitait familièrement dans ma tente,
5 lokacin da Maɗaukaki yana tare da ni, kuma’ya’yana suna kewaye da ni,
quand le Tout-Puissant était encore avec moi, et que mes fils m’entouraient;
6 lokacin da ake zuba madara a inda nake takawa, duwatsu kuma suna ɓulɓulo mini man zaitun.
quand je lavais mes pieds dans le lait, et que le rocher me versait des flots d’huile!
7 “Sa’ad da na je ƙofar birni na zauna a bainin jama’a,
Lorsque je sortais pour me rendre à la porte de la ville, et que j’établissais mon siège sur la place publique,
8 matasan da suka gan ni sukan ja gefe tsofaffi kuma suka tashi tsaye;
en me voyant, les jeunes gens se cachaient, les vieillards se levaient et se tenaient debout.
9 sarakuna suka yi shiru suka rufe bakunansu da hannuwansu;
Les princes retenaient leurs paroles, et mettaient leur main sur la bouche.
10 Muryar manya ta yi tsit harshensu ya manne a rufin bakunansu.
La voix des chefs restait muette, leur langue s’attachait à leur palais.
11 Duk wanda ya ji ni ya yaba mini waɗanda suka gan ni kuma sun amince da ni,
L’oreille qui m’entendait me proclamait heureux, l’œil qui me voyait me rendait témoignage.
12 domin na ceci matalauta waɗanda suka nemi taimako, da marasa mahaifi waɗanda ba su da wanda zai taimake su.
Car je sauvais le pauvre qui implorait du secours, et l’orphelin dénué de tout appui.
13 Mutumin da yake bakin mutuwa ya sa mini albarka. Na faranta wa gwauruwa zuciya.
La bénédiction de celui qui allait périr venait sur moi, je remplissais de joie le cœur de la veuve.
14 Na yafa adalci ya zama suturata; gaskiya ita ce rigata da rawanina.
Je me revêtais de la justice comme d’un vêtement, mon équité était mon manteau et mon turban.
15 Ni ne idon makafi kuma ƙafa ga guragu.
J’étais l’œil de l’aveugle, et le pied du boiteux.
16 Ni mahaifi ne ga masu bukata; na tsaya wa baƙo.
J’étais le père des pauvres, j’examinais avec soin la cause de l’inconnu.
17 Na karya ƙarfin mugaye na ƙwato waɗanda suke riƙe da haƙoransu.
Je brisais la mâchoire de l’injuste, et j’arrachais sa proie d’entre les dents.
18 “Na yi tunani cewa, ‘Zan mutu a cikin gidana, kwanakina da yawa kamar turɓayar ƙasa.
Je disais: « Je mourrai dans mon nid, j’aurai des jours nombreux comme le sable.
19 Jijiyoyina za su kai cikin ruwa, kuma raɓa za tă kwanta a rassana dukan dare.
Mes racines s’étendent vers les eaux, la rosée passe la nuit dans mon feuillage.
20 Ɗaukakata za tă kasance tare da ni garau, bakana koyaushe sabo ne a hannuna.’
Ma gloire reverdira sans cesse, et mon arc reprendra sa vigueur dans ma main. »
21 “Mutane suna mai da hankali su saurare ni, suna yin shiru don su ji shawarata.
On m’écoutait et l’on attendait, on recueillait en silence mon avis.
22 Bayan da na yi magana, ba su ƙara ce kome ba. Maganata ta shige su.
Après que j’avais parlé, personne n’ajoutait rien; ma parole coulait sur eux comme la rosée.
23 Sukan jira ni kamar yadda ake jiran ruwan sama. Sukan sha daga cikin maganganuna kamar mai shan ruwan bazara.
Ils m’attendaient comme on attend la pluie; ils ouvraient la bouche comme aux ondées du printemps.
24 Sa’ad da na yi musu murmushi da ƙyar sukan yarda; hasken fuskata yana da daraja a gare su.
Si je leur souriais, ils ne pouvaient le croire; ils recueillaient avidement ce signe de faveur.
25 Na zaɓar masu inda za su bi na kuma zauna kamar sarkinsu; na zauna kamar sarki a cikin rundunansu; ina nan kamar mai yi wa masu makoki ta’aziyya.
Quand j’allais vers eux, j’avais la première place, je siégeais comme un roi entouré de sa troupe, comme un consolateur au milieu des affligés.