< Ayuba 29 >

1 Ayuba ya ci gaba da jawabinsa,
Also Joob addide, takynge his parable, and seide,
2 “Da ma ina nan lokacin da ya wuce baya can, kwanakin da Allah yake lura da ni,
Who yyueth to me, that I be bisidis the elde monethis, bi the daies in whiche God kepte me?
3 lokacin da fitilarsa take haske a kaina na yi tafiya cikin duhu tare da haskensa.
Whanne his lanterne schynede on myn heed, and Y yede in derknessis at his liyt.
4 Kwanakin da nake tasowa, lokacin da abokantakar Allah ta sa wa gidana albarka,
As Y was in the daies of my yongthe, whanne in priuete God was in my tabernacle.
5 lokacin da Maɗaukaki yana tare da ni, kuma’ya’yana suna kewaye da ni,
Whanne Almyyti God was with me, and my children weren in my cumpas;
6 lokacin da ake zuba madara a inda nake takawa, duwatsu kuma suna ɓulɓulo mini man zaitun.
whanne Y waischide my feet in botere, and the stoon schedde out to me the stremes of oile;
7 “Sa’ad da na je ƙofar birni na zauna a bainin jama’a,
whanne Y yede forth to the yate of the citee, and in the street thei maden redi a chaier to me.
8 matasan da suka gan ni sukan ja gefe tsofaffi kuma suka tashi tsaye;
Yonge men, `that is, wantoun, sien me, and weren hid, and elde men risynge vp stoden;
9 sarakuna suka yi shiru suka rufe bakunansu da hannuwansu;
princes ceessiden to speke, and puttiden the fyngur on her mouth;
10 Muryar manya ta yi tsit harshensu ya manne a rufin bakunansu.
duykis refreyneden her vois, and her tunge cleuyde to her throte.
11 Duk wanda ya ji ni ya yaba mini waɗanda suka gan ni kuma sun amince da ni,
An eere herynge blesside me, and an iye seynge yeldide witnessyng to me;
12 domin na ceci matalauta waɗanda suka nemi taimako, da marasa mahaifi waɗanda ba su da wanda zai taimake su.
for Y hadde delyueride a pore man criynge, and a fadirles child, that hadde noon helpere.
13 Mutumin da yake bakin mutuwa ya sa mini albarka. Na faranta wa gwauruwa zuciya.
The blessyng of a man `to perische cam on me, and Y coumfortide the herte of a widewe.
14 Na yafa adalci ya zama suturata; gaskiya ita ce rigata da rawanina.
Y was clothid with riytfulnesse; and Y clothide me as with a cloth, and with my `doom a diademe.
15 Ni ne idon makafi kuma ƙafa ga guragu.
Y was iye `to a blynde man, and foot to a crokyd man.
16 Ni mahaifi ne ga masu bukata; na tsaya wa baƙo.
Y was a fadir of pore men; and Y enqueride most diligentli the cause, which Y knew not.
17 Na karya ƙarfin mugaye na ƙwato waɗanda suke riƙe da haƙoransu.
Y al tobrak the grete teeth of the wickid man, and Y took awei prey fro hise teeth.
18 “Na yi tunani cewa, ‘Zan mutu a cikin gidana, kwanakina da yawa kamar turɓayar ƙasa.
And Y seide, Y schal die in my nest; and as a palm tre Y schal multiplie daies.
19 Jijiyoyina za su kai cikin ruwa, kuma raɓa za tă kwanta a rassana dukan dare.
My roote is openyde bisidis watris, and deew schal dwelle in my repyng.
20 Ɗaukakata za tă kasance tare da ni garau, bakana koyaushe sabo ne a hannuna.’
My glorie schal euere be renulid, and my bouwe schal be astorid in myn hond.
21 “Mutane suna mai da hankali su saurare ni, suna yin shiru don su ji shawarata.
Thei, that herden me, abiden my sentence; and thei weren ententif, and weren stille to my counsel.
22 Bayan da na yi magana, ba su ƙara ce kome ba. Maganata ta shige su.
Thei dursten no thing adde to my wordis; and my speche droppide on hem.
23 Sukan jira ni kamar yadda ake jiran ruwan sama. Sukan sha daga cikin maganganuna kamar mai shan ruwan bazara.
Thei abididen me as reyn; and thei openyden her mouth as to the softe reyn `comynge late.
24 Sa’ad da na yi musu murmushi da ƙyar sukan yarda; hasken fuskata yana da daraja a gare su.
If ony tyme Y leiyide to hem, thei bileueden not; and the liyt of my cheer felde not doun in to erthe.
25 Na zaɓar masu inda za su bi na kuma zauna kamar sarkinsu; na zauna kamar sarki a cikin rundunansu; ina nan kamar mai yi wa masu makoki ta’aziyya.
If Y wolde go to hem, Y sat the firste; and whanne Y sat as kyng, while the oost stood aboute, netheles Y was comfortour of hem that morenyden.

< Ayuba 29 >