< Ayuba 29 >
1 Ayuba ya ci gaba da jawabinsa,
And Job adds to lift up his allegory and says:
2 “Da ma ina nan lokacin da ya wuce baya can, kwanakin da Allah yake lura da ni,
“Who makes me as [in] months past, As [in] the days of God’s preserving me?
3 lokacin da fitilarsa take haske a kaina na yi tafiya cikin duhu tare da haskensa.
In His causing His lamp to shine on my head, By His light I walk [through] darkness.
4 Kwanakin da nake tasowa, lokacin da abokantakar Allah ta sa wa gidana albarka,
As I have been in days of my maturity, And the counsel of God on my tent.
5 lokacin da Maɗaukaki yana tare da ni, kuma’ya’yana suna kewaye da ni,
When yet the Mighty One [is] with me. Around me—my young ones,
6 lokacin da ake zuba madara a inda nake takawa, duwatsu kuma suna ɓulɓulo mini man zaitun.
When washing my goings with butter, And the firm rock [is] with me—streams of oil.
7 “Sa’ad da na je ƙofar birni na zauna a bainin jama’a,
When I go out to the gate by the city, In a broad place I prepare my seat.
8 matasan da suka gan ni sukan ja gefe tsofaffi kuma suka tashi tsaye;
Youths have seen me, and they have been hidden, And the aged have risen—they stood up.
9 sarakuna suka yi shiru suka rufe bakunansu da hannuwansu;
Princes have kept in words, And they place a hand on their mouth.
10 Muryar manya ta yi tsit harshensu ya manne a rufin bakunansu.
The voice of leaders has been hidden, And their tongue has cleaved to the palate.
11 Duk wanda ya ji ni ya yaba mini waɗanda suka gan ni kuma sun amince da ni,
For the ear heard, and declares me blessed, And the eye has seen, and testifies [to] me.
12 domin na ceci matalauta waɗanda suka nemi taimako, da marasa mahaifi waɗanda ba su da wanda zai taimake su.
For I deliver the afflicted who is crying, And the fatherless who has no helper.
13 Mutumin da yake bakin mutuwa ya sa mini albarka. Na faranta wa gwauruwa zuciya.
The blessing of the perishing comes on me, And I cause the heart of the widow to sing.
14 Na yafa adalci ya zama suturata; gaskiya ita ce rigata da rawanina.
I have put on righteousness, and it clothes me, My justice as a robe and a crown.
15 Ni ne idon makafi kuma ƙafa ga guragu.
I have been eyes to the blind, And I [am] feet to the lame.
16 Ni mahaifi ne ga masu bukata; na tsaya wa baƙo.
I [am] a father to the needy, And the cause I have not known I search out.
17 Na karya ƙarfin mugaye na ƙwato waɗanda suke riƙe da haƙoransu.
And I break the jaw-teeth of the perverse, And from his teeth I cast away prey.
18 “Na yi tunani cewa, ‘Zan mutu a cikin gidana, kwanakina da yawa kamar turɓayar ƙasa.
And I say, I expire with my nest, And I multiply days as the sand.
19 Jijiyoyina za su kai cikin ruwa, kuma raɓa za tă kwanta a rassana dukan dare.
My root is open to the waters, And dew lodges on my branch.
20 Ɗaukakata za tă kasance tare da ni garau, bakana koyaushe sabo ne a hannuna.’
My glory [is] fresh with me, And my bow is renewed in my hand.
21 “Mutane suna mai da hankali su saurare ni, suna yin shiru don su ji shawarata.
They have listened to me, Indeed, they wait, and are silent for my counsel.
22 Bayan da na yi magana, ba su ƙara ce kome ba. Maganata ta shige su.
After my word they do not change, And my speech drops on them,
23 Sukan jira ni kamar yadda ake jiran ruwan sama. Sukan sha daga cikin maganganuna kamar mai shan ruwan bazara.
And they wait for me as [for] rain, And they have opened wide their mouth [As] for the spring rain.
24 Sa’ad da na yi musu murmushi da ƙyar sukan yarda; hasken fuskata yana da daraja a gare su.
I laugh at them—they give no credence, And do not cause the light of my face to fall.
25 Na zaɓar masu inda za su bi na kuma zauna kamar sarkinsu; na zauna kamar sarki a cikin rundunansu; ina nan kamar mai yi wa masu makoki ta’aziyya.
I choose their way, and sit [as] head, And I dwell as a king in a troop, When he comforts mourners.”