< Ayuba 29 >

1 Ayuba ya ci gaba da jawabinsa,
Job also added, taking up his parable, and said:
2 “Da ma ina nan lokacin da ya wuce baya can, kwanakin da Allah yake lura da ni,
Who will grant me, that I might be according to the months past, according to the days in which God kept me?
3 lokacin da fitilarsa take haske a kaina na yi tafiya cikin duhu tare da haskensa.
When his lamp shined over my head, and I walked by his light in darkness?
4 Kwanakin da nake tasowa, lokacin da abokantakar Allah ta sa wa gidana albarka,
As I was in the days of my youth, when God was secretly in my tabernacle?
5 lokacin da Maɗaukaki yana tare da ni, kuma’ya’yana suna kewaye da ni,
When the Almighty was with me: and my servants round about me?
6 lokacin da ake zuba madara a inda nake takawa, duwatsu kuma suna ɓulɓulo mini man zaitun.
When I washed my feet with butter, and the rock poured me out rivers of oil?
7 “Sa’ad da na je ƙofar birni na zauna a bainin jama’a,
When I went out to the gate of the city, and in the street they prepared me a chair?
8 matasan da suka gan ni sukan ja gefe tsofaffi kuma suka tashi tsaye;
The young men saw me, and hid themselves: and the old men rose up and stood.
9 sarakuna suka yi shiru suka rufe bakunansu da hannuwansu;
The princes ceased to speak, and laid the finger on their mouth.
10 Muryar manya ta yi tsit harshensu ya manne a rufin bakunansu.
The rulers held their peace, and their tongue cleaved to their throat.
11 Duk wanda ya ji ni ya yaba mini waɗanda suka gan ni kuma sun amince da ni,
The ear that heard me blessed me, and the eye that saw me gave witness to me:
12 domin na ceci matalauta waɗanda suka nemi taimako, da marasa mahaifi waɗanda ba su da wanda zai taimake su.
Because I had delivered the poor man that cried out; and the fatherless that had no helper.
13 Mutumin da yake bakin mutuwa ya sa mini albarka. Na faranta wa gwauruwa zuciya.
The blessing of him that was ready to perish came upon me, and I comforted the heart of the widow.
14 Na yafa adalci ya zama suturata; gaskiya ita ce rigata da rawanina.
I was clad with justice: and I clothed myself with my judgment, as with a robe and a diadem.
15 Ni ne idon makafi kuma ƙafa ga guragu.
I was an eye to the blind, and a foot to the lame.
16 Ni mahaifi ne ga masu bukata; na tsaya wa baƙo.
I was the father of the poor: and the cause which I knew not, I searched out most diligently.
17 Na karya ƙarfin mugaye na ƙwato waɗanda suke riƙe da haƙoransu.
I broke the jaws of the wicked man, and out of his teeth I took away the prey.
18 “Na yi tunani cewa, ‘Zan mutu a cikin gidana, kwanakina da yawa kamar turɓayar ƙasa.
And I said: I shall die in my nest, and as a palm tree shall multiply my days.
19 Jijiyoyina za su kai cikin ruwa, kuma raɓa za tă kwanta a rassana dukan dare.
My root is opened beside the waters, and dew shall continue in my harvest.
20 Ɗaukakata za tă kasance tare da ni garau, bakana koyaushe sabo ne a hannuna.’
My glory shall always be renewed, and my bow in my hand shall be repaired.
21 “Mutane suna mai da hankali su saurare ni, suna yin shiru don su ji shawarata.
They that heard me, waited for my sentence, and being attentive held their peace at my counsel.
22 Bayan da na yi magana, ba su ƙara ce kome ba. Maganata ta shige su.
To my words they durst add nothing, and my speech dropped upon them.
23 Sukan jira ni kamar yadda ake jiran ruwan sama. Sukan sha daga cikin maganganuna kamar mai shan ruwan bazara.
They waited for me as for rain, and they opened their mouth as for a latter shower.
24 Sa’ad da na yi musu murmushi da ƙyar sukan yarda; hasken fuskata yana da daraja a gare su.
If at any time I laughed on them, they believed not, and the light of my countenance fell not on earth.
25 Na zaɓar masu inda za su bi na kuma zauna kamar sarkinsu; na zauna kamar sarki a cikin rundunansu; ina nan kamar mai yi wa masu makoki ta’aziyya.
If I had a mind to go to them, I sat first, and when I sat as a king, with his army standing about him, yet I was a comforter of them that mourned.

< Ayuba 29 >