< Ayuba 29 >

1 Ayuba ya ci gaba da jawabinsa,
Job vervolgde zijn rede, en sprak
2 “Da ma ina nan lokacin da ya wuce baya can, kwanakin da Allah yake lura da ni,
Ach, was ik als in vroeger maanden, In de tijd, toen God mij behoedde,
3 lokacin da fitilarsa take haske a kaina na yi tafiya cikin duhu tare da haskensa.
Toen Hij zijn lamp boven mijn hoofd liet stralen, En ik bij zijn licht door de duisternis ging;
4 Kwanakin da nake tasowa, lokacin da abokantakar Allah ta sa wa gidana albarka,
Zoals ik was in mijn beste dagen Toen God mijn tent nog beschutte!
5 lokacin da Maɗaukaki yana tare da ni, kuma’ya’yana suna kewaye da ni,
Toen de Almachtige nog met mij was, Mijn kinderen mij nog omringden;
6 lokacin da ake zuba madara a inda nake takawa, duwatsu kuma suna ɓulɓulo mini man zaitun.
Toen mijn voeten zich baadden in boter, De rots, waar ik stond, beken olie liet stromen;
7 “Sa’ad da na je ƙofar birni na zauna a bainin jama’a,
Als ik uitging naar de poort van de stad, En op het plein mijn zetel liet zetten:
8 matasan da suka gan ni sukan ja gefe tsofaffi kuma suka tashi tsaye;
Trokken de jongemannen zich terug, zodra ze mij zagen, Rezen de grijsaards op en bleven staan,
9 sarakuna suka yi shiru suka rufe bakunansu da hannuwansu;
Staakten de edelen hun gesprek En legden de hand op hun mond.
10 Muryar manya ta yi tsit harshensu ya manne a rufin bakunansu.
De stem der leiders verstomde, Hun tong kleefde aan hun gehemelte vast;
11 Duk wanda ya ji ni ya yaba mini waɗanda suka gan ni kuma sun amince da ni,
Toen het oor, dat het hoorde, mij gelukkig prees En het oog, dat het zag, mij bijval schonk!
12 domin na ceci matalauta waɗanda suka nemi taimako, da marasa mahaifi waɗanda ba su da wanda zai taimake su.
Want ik hielp den arme, die om bijstand riep, Den wees, die geen helper meer had;
13 Mutumin da yake bakin mutuwa ya sa mini albarka. Na faranta wa gwauruwa zuciya.
Dien de ondergang dreigde, zegende mij, Het hart der weduwe vrolijkte ik op;
14 Na yafa adalci ya zama suturata; gaskiya ita ce rigata da rawanina.
Rechtschapenheid trok ik aan als een kleed, Mijn gerechtigheid als een mantel en kroon.
15 Ni ne idon makafi kuma ƙafa ga guragu.
Ik was de ogen voor blinden, De voeten voor kreupelen;
16 Ni mahaifi ne ga masu bukata; na tsaya wa baƙo.
Voor armen was ik een vader, Voor onbekenden onderzocht ik het pleit.
17 Na karya ƙarfin mugaye na ƙwato waɗanda suke riƙe da haƙoransu.
Maar den boosdoener brak ik de tanden, En rukte hem de prooi uit zijn kaken.
18 “Na yi tunani cewa, ‘Zan mutu a cikin gidana, kwanakina da yawa kamar turɓayar ƙasa.
Ik dacht bij mijzelf: Oud zal ik sterven Mijn dagen zullen talrijk zijn als het zand;
19 Jijiyoyina za su kai cikin ruwa, kuma raɓa za tă kwanta a rassana dukan dare.
Mijn wortel zal openstaan voor het water, De dauw op mijn takken vernachten;
20 Ɗaukakata za tă kasance tare da ni garau, bakana koyaushe sabo ne a hannuna.’
Mijn eer blijft steeds nieuw, Mijn boog wint aan jeugdige kracht in mijn hand!
21 “Mutane suna mai da hankali su saurare ni, suna yin shiru don su ji shawarata.
Ze luisterden zwijgend naar mij En wachtten mijn beslissing af;
22 Bayan da na yi magana, ba su ƙara ce kome ba. Maganata ta shige su.
Had ik uitgesproken, dan nam niemand het woord, Maar mijn rede druppelde op hen neer.
23 Sukan jira ni kamar yadda ake jiran ruwan sama. Sukan sha daga cikin maganganuna kamar mai shan ruwan bazara.
Ze verlangden naar mij als naar regen, Met open mond als naar een late bui.
24 Sa’ad da na yi musu murmushi da ƙyar sukan yarda; hasken fuskata yana da daraja a gare su.
Lachte ik hun toe, ze durfden het niet geloven, En vingen het stralen van mijn aangezicht op.
25 Na zaɓar masu inda za su bi na kuma zauna kamar sarkinsu; na zauna kamar sarki a cikin rundunansu; ina nan kamar mai yi wa masu makoki ta’aziyya.
Bezocht ik hen, ik zat bovenaan, Troonde als een vorst bij zijn troepen, als een die treurenden troost.

< Ayuba 29 >