< Ayuba 28 >

1 Akwai ramin azurfa akwai kuma wurin da ake tace zinariya.
Ciertamente la plata tiene su oculto nacimiento, y el oro lugar de donde lo sacan.
2 Daga cikin ƙasa ake ciro ƙarfe, ana kuma narkar da tagulla daga cikin dutse.
El hierro es tomado del polvo, y de la piedra es fundido el metal.
3 Mutum ya kawo ƙarshen duhu; yakan bincike zuzzurfar iyaka, yana neman duwatsu a wuri mafi duhu.
A las tinieblas puso término, y a toda obra perfecta que él hizo puso piedra de oscuridad y de sombra de muerte.
4 Nesa da inda mutane suke zama, yakan huda rami yă yi abin lilo, a wurin da mutane ba sa bi.
Sale el río junto al morador; y las aguas sin pie, más altas que el hombre, se fueron.
5 Cikin ƙasa inda ake samun abinci, a ƙarƙashinta kuwa zafi ne kamar wuta;
Tierra de la cual saldrá pan, y debajo de ella estará como convertida en fuego.
6 akwai duwatsu masu daraja a cikin duwatsunta, akwai kuma zinariya a cikin ƙurarta.
Lugar que sus piedras serán zafiros, y tendrá polvos de oro.
7 Tsuntsu mai farauta bai san hanyarta ba, ba shahon da ya taɓa ganin ta.
Senda que nunca la conoció ave, ni ojo de buitre la vio.
8 Manyan namun jeji ba su taɓa binta ba, ba zakin da ya taɓa binta.
Nunca la pisaron animales fieros, ni pasó por ella león.
9 Hannun mutum ya iya sarrafa ƙanƙarar duwatsu, yă kuma tumɓuke tushen duwatsu.
En el pedernal puso su mano, y trastornó los montes de raíz.
10 Yana tona rami a cikin duwatsu idanunsa suna ganin dukan dukiyar da ke cikin duwatsun.
De los peñascos cortó ríos, y todo lo precioso vio su ojo.
11 Yana nema daga ina ruwan rafi yake ɓulɓulowa yana kuma binciko abubuwan da suke a ɓoye yă kawo su cikin haske.
Los ríos detuvo en su nacimiento, y lo escondido hizo salir a luz.
12 Amma a ina ne za a iya samun hikima? Ina fahimta take zama?
¿Mas la sabiduría, donde se hallará? ¿y el lugar de la prudencia, donde está?
13 Mutum bai gane muhimmancinta ba, ba a samunta a ƙasar masu rai.
Nunca el hombre supo su valor, ni se halla en la tierra de los vivientes.
14 Zurfi ya ce, “Ba ta wurina”; teku ya ce, “Ba ta wurina.”
El abismo dice: No está en mí: y la mar dijo: Ni conmigo.
15 Ba irin zinariyar da za tă iya sayenta, ko kuma a iya auna nauyinta da azurfa.
No se dará por oro, ni su precio será a peso de plata.
16 Ba za a iya sayenta da zinariyar Ofir, ko sauran duwatsu masu daraja ba.
No es apreciada con oro de Ofir, ni con ónix precioso, ni con zafiro.
17 Zinariya da madubi ba za su iya gwada kansu da ita ba, ba kuwa za a iya musayarta da abubuwan da aka yi da zinariya ba.
El oro no se le igualará, ni el diamante; ni se trocará por vaso de oro fino.
18 Kada ma a ce murjani da duwatsu masu walƙiya; farashin hikima ya fi na lu’ulu’ai.
De coral, ni de gabis, no se hará mención: la sabiduría es mejor que piedras preciosas.
19 Ba za a iya daidaita darajarta da duwatsun Tofaz na Kush ba, zallar zinariya ma ba tă isa ta saye ta ba.
No se igualará con ella esmeralda de Etiopía: no se podrá apreciar con oro fino.
20 “To, daga ina ke nan hikima ta fito? Ina fahimta take zama?
¿De dónde, pues, vendrá la sabiduría? ¿y dónde está el lugar de la inteligencia?
21 An ɓoye ta daga idanun kowane abu mai rai, har tsuntsayen sararin sama ma an ɓoye masu ita.
Pues es encubierta a los ojos de todo viviente, y a toda ave del cielo es oculta.
22 Hallaka da mutuwa suna cewa, ‘Jita-jitarta kaɗai muke ji.’
La perdición y la muerte dijeron: Su fama hemos escuchado con nuestros oídos.
23 Allah ya gane hanyar zuwa wurinta. Shi ne kaɗai ya san inda take zama,
Dios entendió su camino, y él solo conoció su lugar.
24 Gama yana ganin iyakar duniya kuma yana ganin duk abin da yake ƙarƙashin sama.
Porque él mira hasta los fines de la tierra, y ve debajo de todo el cielo:
25 Lokacin da ya yi iska ya sa ta hura, ya kuma auna ruwaye.
Haciendo peso al viento, y poniendo las aguas por medida.
26 Lokacin da ya yi wa ruwan sama doka da kuma hanya domin walƙiya,
Cuando él hizo ley a la lluvia, y camino al relámpago de los truenos:
27 sai ya dubi hikima ya auna ta; ya tabbatar da ita, ya gwada ta.
Entonces la vio él, y la manifestó; la preparó, y también la inquirió.
28 Ya kuma ce wa mutum, ‘Tsoron Ubangiji shi ne hikima, kuma guje wa mugunta shi ne fahimi.’”
Y dijo al hombre: He aquí, que el temor del Señor es la sabiduría; y la inteligencia el apartarse del mal.

< Ayuba 28 >