< Ayuba 28 >

1 Akwai ramin azurfa akwai kuma wurin da ake tace zinariya.
Tiešām, sudrabam ir savi ceļi, kur tas rodas, un kausējamam zeltam sava vieta.
2 Daga cikin ƙasa ake ciro ƙarfe, ana kuma narkar da tagulla daga cikin dutse.
Dzelzs no zemes top ņemta, un no akmeņiem varš top kausēts.
3 Mutum ya kawo ƙarshen duhu; yakan bincike zuzzurfar iyaka, yana neman duwatsu a wuri mafi duhu.
Tumsai gals likts, un caur caurim cilvēks izmeklē arī pašā galējā tumsā apslēptos akmeņus.
4 Nesa da inda mutane suke zama, yakan huda rami yă yi abin lilo, a wurin da mutane ba sa bi.
Viņš izrok ceļu turp, kur neviens nedzīvo, un kur neviena kāja neved; tur viņš karājās un nolaižās tālu no cilvēkiem.
5 Cikin ƙasa inda ake samun abinci, a ƙarƙashinta kuwa zafi ne kamar wuta;
No zemes virsas izaug maize, viņas apakša top apgriezta kā no uguns.
6 akwai duwatsu masu daraja a cikin duwatsunta, akwai kuma zinariya a cikin ƙurarta.
Viņas akmeņos ir safīri, un tur rodas zelta graudi.
7 Tsuntsu mai farauta bai san hanyarta ba, ba shahon da ya taɓa ganin ta.
Ne ērglis šo ceļu nav ieraudzījis, ne vanaga acs to nav redzējusi.
8 Manyan namun jeji ba su taɓa binta ba, ba zakin da ya taɓa binta.
Briesmīgi zvēri pa to nav gājuši, un lauva pa to nav staigājis.
9 Hannun mutum ya iya sarrafa ƙanƙarar duwatsu, yă kuma tumɓuke tushen duwatsu.
Cilvēks pieliek savu roku pie akmeņiem, un izrok kalnu pamatus;
10 Yana tona rami a cikin duwatsu idanunsa suna ganin dukan dukiyar da ke cikin duwatsun.
Viņš izcērt ceļus akmeņu kalnos, un viņa acs ierauga visādus dārgumus;
11 Yana nema daga ina ruwan rafi yake ɓulɓulowa yana kuma binciko abubuwan da suke a ɓoye yă kawo su cikin haske.
Viņš aizdara ūdeņus, kā nesūcās cauri, un izved gaismā, kas ir apslēpts.
12 Amma a ina ne za a iya samun hikima? Ina fahimta take zama?
Bet gudrību, kur to atrod, un kur mājo atzīšana?
13 Mutum bai gane muhimmancinta ba, ba a samunta a ƙasar masu rai.
Cilvēks nezin, ar ko lai to pērk un dzīvo zemē to nevar uziet.
14 Zurfi ya ce, “Ba ta wurina”; teku ya ce, “Ba ta wurina.”
Bezdibenis saka: te viņas nav; un jūra saka: tā nav pie manis.
15 Ba irin zinariyar da za tă iya sayenta, ko kuma a iya auna nauyinta da azurfa.
Zeltu par viņu nevar dot, nedz sudraba maksu par viņu iesvērt.
16 Ba za a iya sayenta da zinariyar Ofir, ko sauran duwatsu masu daraja ba.
To nevar uzsvērt ar Ofira zeltu nedz ar dārgiem oniksa un safīra akmeņiem.
17 Zinariya da madubi ba za su iya gwada kansu da ita ba, ba kuwa za a iya musayarta da abubuwan da aka yi da zinariya ba.
To neatsver ne zelts, ne spīdoši akmeņi, to nevar izmīt pret zelta glītumiem.
18 Kada ma a ce murjani da duwatsu masu walƙiya; farashin hikima ya fi na lu’ulu’ai.
Par pērlēm un kristālu nav ko runāt; jo gudrību mantot ir pārāki par pērlēm.
19 Ba za a iya daidaita darajarta da duwatsun Tofaz na Kush ba, zallar zinariya ma ba tă isa ta saye ta ba.
Moru zemes topāzs viņai nav līdzīgs, un visu šķīstais zelts viņu nepanāk.
20 “To, daga ina ke nan hikima ta fito? Ina fahimta take zama?
Nu tad, no kurienes nāk gudrība un kur mājo atzīšana?
21 An ɓoye ta daga idanun kowane abu mai rai, har tsuntsayen sararin sama ma an ɓoye masu ita.
Jo tā ir apslēpta priekš visu acīm, kas dzīvo, un putniem apakš debess tā ir nezināma.
22 Hallaka da mutuwa suna cewa, ‘Jita-jitarta kaɗai muke ji.’
Elle un nāve saka: ar savām ausīm gan esam dzirdējuši viņas slavu.
23 Allah ya gane hanyar zuwa wurinta. Shi ne kaɗai ya san inda take zama,
Dievs pazīst viņas ceļu, un Tas zin viņas vietu.
24 Gama yana ganin iyakar duniya kuma yana ganin duk abin da yake ƙarƙashin sama.
Jo Viņš skatās līdz pasaules galiem, Viņš redz, kas apakš visām debesīm.
25 Lokacin da ya yi iska ya sa ta hura, ya kuma auna ruwaye.
Kad Viņš vējam deva savu svaru un ūdeni nosvēra pēc mēra,
26 Lokacin da ya yi wa ruwan sama doka da kuma hanya domin walƙiya,
Kad Viņš lietum sprieda likumu un zibenim un pērkonam ceļu,
27 sai ya dubi hikima ya auna ta; ya tabbatar da ita, ya gwada ta.
Tad Viņš to izredzēja un to izteica, Viņš to sataisīja un izdibināja,
28 Ya kuma ce wa mutum, ‘Tsoron Ubangiji shi ne hikima, kuma guje wa mugunta shi ne fahimi.’”
Un sacīja uz cilvēku: redzi, Tā Kunga bijāšana, tā ir gudrība, un atstāties no ļauna, tā ir atzīšana.

< Ayuba 28 >