< Ayuba 28 >
1 Akwai ramin azurfa akwai kuma wurin da ake tace zinariya.
habet argentum venarum suarum principia et auro locus est in quo conflatur
2 Daga cikin ƙasa ake ciro ƙarfe, ana kuma narkar da tagulla daga cikin dutse.
ferrum de terra tollitur et lapis solutus calore in aes vertitur
3 Mutum ya kawo ƙarshen duhu; yakan bincike zuzzurfar iyaka, yana neman duwatsu a wuri mafi duhu.
tempus posuit tenebris et universorum finem ipse considerat lapidem quoque caliginis et umbram mortis
4 Nesa da inda mutane suke zama, yakan huda rami yă yi abin lilo, a wurin da mutane ba sa bi.
dividit torrens a populo peregrinante eos quos oblitus est pes egentis hominum et invios
5 Cikin ƙasa inda ake samun abinci, a ƙarƙashinta kuwa zafi ne kamar wuta;
terra de qua oriebatur panis in loco suo igne subversa est
6 akwai duwatsu masu daraja a cikin duwatsunta, akwai kuma zinariya a cikin ƙurarta.
locus sapphyri lapides eius et glebae illius aurum
7 Tsuntsu mai farauta bai san hanyarta ba, ba shahon da ya taɓa ganin ta.
semitam ignoravit avis nec intuitus est oculus vulturis
8 Manyan namun jeji ba su taɓa binta ba, ba zakin da ya taɓa binta.
non calcaverunt eam filii institorum nec pertransivit per eam leaena
9 Hannun mutum ya iya sarrafa ƙanƙarar duwatsu, yă kuma tumɓuke tushen duwatsu.
ad silicem extendit manum suam subvertit a radicibus montes
10 Yana tona rami a cikin duwatsu idanunsa suna ganin dukan dukiyar da ke cikin duwatsun.
in petris rivos excidit et omne pretiosum vidit oculus eius
11 Yana nema daga ina ruwan rafi yake ɓulɓulowa yana kuma binciko abubuwan da suke a ɓoye yă kawo su cikin haske.
profunda quoque fluviorum scrutatus est et abscondita produxit in lucem
12 Amma a ina ne za a iya samun hikima? Ina fahimta take zama?
sapientia vero ubi invenitur et quis est locus intellegentiae
13 Mutum bai gane muhimmancinta ba, ba a samunta a ƙasar masu rai.
nescit homo pretium eius nec invenitur in terra suaviter viventium
14 Zurfi ya ce, “Ba ta wurina”; teku ya ce, “Ba ta wurina.”
abyssus dicit non est in me et mare loquitur non est mecum
15 Ba irin zinariyar da za tă iya sayenta, ko kuma a iya auna nauyinta da azurfa.
non dabitur aurum obrizum pro ea nec adpendetur argentum in commutatione eius
16 Ba za a iya sayenta da zinariyar Ofir, ko sauran duwatsu masu daraja ba.
non conferetur tinctis Indiae coloribus nec lapidi sardonico pretiosissimo vel sapphyro
17 Zinariya da madubi ba za su iya gwada kansu da ita ba, ba kuwa za a iya musayarta da abubuwan da aka yi da zinariya ba.
non adaequabitur ei aurum vel vitrum nec commutabuntur pro ea vasa auri
18 Kada ma a ce murjani da duwatsu masu walƙiya; farashin hikima ya fi na lu’ulu’ai.
excelsa et eminentia non memorabuntur conparatione eius trahitur autem sapientia de occultis
19 Ba za a iya daidaita darajarta da duwatsun Tofaz na Kush ba, zallar zinariya ma ba tă isa ta saye ta ba.
non adaequabitur ei topazium de Aethiopia nec tincturae mundissimae conponetur
20 “To, daga ina ke nan hikima ta fito? Ina fahimta take zama?
unde ergo sapientia veniet et quis est locus intellegentiae
21 An ɓoye ta daga idanun kowane abu mai rai, har tsuntsayen sararin sama ma an ɓoye masu ita.
abscondita est ab oculis omnium viventium volucres quoque caeli latet
22 Hallaka da mutuwa suna cewa, ‘Jita-jitarta kaɗai muke ji.’
perditio et mors dixerunt auribus nostris audivimus famam eius
23 Allah ya gane hanyar zuwa wurinta. Shi ne kaɗai ya san inda take zama,
Deus intellegit viam eius et ipse novit locum illius
24 Gama yana ganin iyakar duniya kuma yana ganin duk abin da yake ƙarƙashin sama.
ipse enim fines mundi intuetur et omnia quae sub caelo sunt respicit
25 Lokacin da ya yi iska ya sa ta hura, ya kuma auna ruwaye.
qui fecit ventis pondus et aquas adpendit mensura
26 Lokacin da ya yi wa ruwan sama doka da kuma hanya domin walƙiya,
quando ponebat pluviis legem et viam procellis sonantibus
27 sai ya dubi hikima ya auna ta; ya tabbatar da ita, ya gwada ta.
tunc vidit illam et enarravit et praeparavit et investigavit
28 Ya kuma ce wa mutum, ‘Tsoron Ubangiji shi ne hikima, kuma guje wa mugunta shi ne fahimi.’”
et dixit homini ecce timor Domini ipsa est sapientia et recedere a malo intellegentia