< Ayuba 28 >
1 Akwai ramin azurfa akwai kuma wurin da ake tace zinariya.
Denn für das Silber gibt es einen Fundort, und eine Stätte für das Gold, das man läutert.
2 Daga cikin ƙasa ake ciro ƙarfe, ana kuma narkar da tagulla daga cikin dutse.
Eisen wird hervorgeholt aus der Erde, und Gestein schmelzt man zu Kupfer.
3 Mutum ya kawo ƙarshen duhu; yakan bincike zuzzurfar iyaka, yana neman duwatsu a wuri mafi duhu.
Er hat der Finsternis ein Ende gesetzt, und durchforscht bis zur äußersten Grenze das Gestein der Finsternis und des Todesschattens.
4 Nesa da inda mutane suke zama, yakan huda rami yă yi abin lilo, a wurin da mutane ba sa bi.
Er bricht einen Schacht fern von dem Wohnenden; die von dem Fuße Vergessenen hangen hinab, fern von den Menschen schweben sie.
5 Cikin ƙasa inda ake samun abinci, a ƙarƙashinta kuwa zafi ne kamar wuta;
Die Erde, aus ihr kommt Brot hervor, und ihr Unteres wird zerwühlt wie vom Feuer.
6 akwai duwatsu masu daraja a cikin duwatsunta, akwai kuma zinariya a cikin ƙurarta.
Ihr Gestein ist der Sitz des Saphirs, und Goldstufen sind darin.
7 Tsuntsu mai farauta bai san hanyarta ba, ba shahon da ya taɓa ganin ta.
Ein Pfad, den der Raubvogel nicht kennt, und den das Auge des Habichts nicht erblickt hat;
8 Manyan namun jeji ba su taɓa binta ba, ba zakin da ya taɓa binta.
den die wilden Tiere nicht betreten, über den der Löwe nicht hingeschritten ist.
9 Hannun mutum ya iya sarrafa ƙanƙarar duwatsu, yă kuma tumɓuke tushen duwatsu.
Er legt seine Hand an das harte Gestein, wühlt die Berge um von der Wurzel aus.
10 Yana tona rami a cikin duwatsu idanunsa suna ganin dukan dukiyar da ke cikin duwatsun.
Kanäle haut er durch die Felsen, und allerlei Köstliches sieht sein Auge.
11 Yana nema daga ina ruwan rafi yake ɓulɓulowa yana kuma binciko abubuwan da suke a ɓoye yă kawo su cikin haske.
Er dämmt Flüsse ein, daß sie nicht durchsickern, und Verborgenes zieht er hervor an das Licht.
12 Amma a ina ne za a iya samun hikima? Ina fahimta take zama?
Aber die Weisheit, wo wird sie erlangt? Und welches ist die Stätte des Verstandes?
13 Mutum bai gane muhimmancinta ba, ba a samunta a ƙasar masu rai.
Kein Mensch kennt ihren Wert, und im Lande der Lebendigen wird sie nicht gefunden.
14 Zurfi ya ce, “Ba ta wurina”; teku ya ce, “Ba ta wurina.”
Die Tiefe spricht: Sie ist nicht in mir, und das Meer spricht: Sie ist nicht bei mir.
15 Ba irin zinariyar da za tă iya sayenta, ko kuma a iya auna nauyinta da azurfa.
Geläutertes Gold kann nicht für sie gegeben, und Silber nicht dargewogen werden als ihr Kaufpreis.
16 Ba za a iya sayenta da zinariyar Ofir, ko sauran duwatsu masu daraja ba.
Sie wird nicht aufgewogen mit Gold von Ophir, mit kostbarem Onyx und Saphir.
17 Zinariya da madubi ba za su iya gwada kansu da ita ba, ba kuwa za a iya musayarta da abubuwan da aka yi da zinariya ba.
Gold und Glas kann man ihr nicht gleichstellen, noch sie eintauschen gegen ein Gerät von gediegenem Golde.
18 Kada ma a ce murjani da duwatsu masu walƙiya; farashin hikima ya fi na lu’ulu’ai.
Korallen und Kristall kommen neben ihr nicht in Erwähnung; und der Besitz der Weisheit ist mehr wert als Perlen.
19 Ba za a iya daidaita darajarta da duwatsun Tofaz na Kush ba, zallar zinariya ma ba tă isa ta saye ta ba.
Nicht kann man ihr gleichstellen den Topas von Äthiopien; mit feinem Golde wird sie nicht aufgewogen.
20 “To, daga ina ke nan hikima ta fito? Ina fahimta take zama?
Die Weisheit nun, woher kommt sie, und welches ist die Stätte des Verstandes?
21 An ɓoye ta daga idanun kowane abu mai rai, har tsuntsayen sararin sama ma an ɓoye masu ita.
Denn sie ist verborgen vor den Augen aller Lebendigen, und vor den Vögeln des Himmels ist sie verhüllt.
22 Hallaka da mutuwa suna cewa, ‘Jita-jitarta kaɗai muke ji.’
Der Abgrund und der Tod sagen: Mit unseren Ohren haben wir ein Gerücht von ihr gehört.
23 Allah ya gane hanyar zuwa wurinta. Shi ne kaɗai ya san inda take zama,
Gott versteht ihren Weg, und er kennt ihre Stätte.
24 Gama yana ganin iyakar duniya kuma yana ganin duk abin da yake ƙarƙashin sama.
Denn er schaut bis zu den Enden der Erde; unter dem ganzen Himmel sieht er.
25 Lokacin da ya yi iska ya sa ta hura, ya kuma auna ruwaye.
Als er dem Winde ein Gewicht bestimmte, und die Wasser mit dem Maße abwog,
26 Lokacin da ya yi wa ruwan sama doka da kuma hanya domin walƙiya,
als er dem Regen ein Gesetz bestimmte und eine Bahn dem Donnerstrahl:
27 sai ya dubi hikima ya auna ta; ya tabbatar da ita, ya gwada ta.
da sah er sie und tat sie kund, er setzte sie ein und durchforschte sie auch.
28 Ya kuma ce wa mutum, ‘Tsoron Ubangiji shi ne hikima, kuma guje wa mugunta shi ne fahimi.’”
Und zu dem Menschen sprach er: Siehe, die Furcht des Herrn ist Weisheit, und vom Bösen weichen ist Verstand.