< Ayuba 28 >
1 Akwai ramin azurfa akwai kuma wurin da ake tace zinariya.
Il y a des contrées où naît l'argent, d'autres où l'on épure l'or.
2 Daga cikin ƙasa ake ciro ƙarfe, ana kuma narkar da tagulla daga cikin dutse.
Le fer se tire du sol, et l'airain, semblable à de la pierre, est extrait des mines.
3 Mutum ya kawo ƙarshen duhu; yakan bincike zuzzurfar iyaka, yana neman duwatsu a wuri mafi duhu.
Le Seigneur a réglé les ténèbres; il maintient ponctuellement les limites qu'il a tracées; la roche sombre se distingue de l'ombre de la mort,
4 Nesa da inda mutane suke zama, yakan huda rami yă yi abin lilo, a wurin da mutane ba sa bi.
Le lit du torrent d'un amas de poussière; ceux qui abandonnent leur chemin s'affaiblissent, ils sont rejetés du reste des mortels.
5 Cikin ƙasa inda ake samun abinci, a ƙarƙashinta kuwa zafi ne kamar wuta;
Le fond du sol d'où sortira le pain a été tourmenté comme du feu.
6 akwai duwatsu masu daraja a cikin duwatsunta, akwai kuma zinariya a cikin ƙurarta.
Parmi ses pierres on trouve le saphir, et il y a là aussi des amas d'or.
7 Tsuntsu mai farauta bai san hanyarta ba, ba shahon da ya taɓa ganin ta.
Le sentier? L'oiseau ne l'a pas connu; l'œil du vautour ne s'y est point arrêté.
8 Manyan namun jeji ba su taɓa binta ba, ba zakin da ya taɓa binta.
Les fils des vaniteux n'y ont point porté leurs pas; le lion n'a point passé auprès.
9 Hannun mutum ya iya sarrafa ƙanƙarar duwatsu, yă kuma tumɓuke tushen duwatsu.
L'homme a étendu sa main jusqu'à la cime des monts, il a ouvert leurs racines.
10 Yana tona rami a cikin duwatsu idanunsa suna ganin dukan dukiyar da ke cikin duwatsun.
Il a fendu le tourbillon des fleuves, et mon œil a vu ce qu'il y a de précieux.
11 Yana nema daga ina ruwan rafi yake ɓulɓulowa yana kuma binciko abubuwan da suke a ɓoye yă kawo su cikin haske.
L'homme a exploré le fond des rivières, et il a mis au jour sa puissance.
12 Amma a ina ne za a iya samun hikima? Ina fahimta take zama?
Mais la sagesse, où est-elle trouvée? où la science réside-t-elle?
13 Mutum bai gane muhimmancinta ba, ba a samunta a ƙasar masu rai.
L'homme n'en sait pas le chemin, nul des mortels ne l'a découvert.
14 Zurfi ya ce, “Ba ta wurina”; teku ya ce, “Ba ta wurina.”
L'abîme dit: Elle n'est point en moi; la mer a dit: Elle n'est pas avec moi.
15 Ba irin zinariyar da za tă iya sayenta, ko kuma a iya auna nauyinta da azurfa.
On ne l'obtient pas au prix de trésors; elle ne s'échange pas contre de l'argent.
16 Ba za a iya sayenta da zinariyar Ofir, ko sauran duwatsu masu daraja ba.
On ne la mettra point dans la balance avec de l'or d'Ophir, des saphirs et des onyx.
17 Zinariya da madubi ba za su iya gwada kansu da ita ba, ba kuwa za a iya musayarta da abubuwan da aka yi da zinariya ba.
Ni l'or ni le cristal ne la vaudront; on ne lui égalera pas des vases d'or.
18 Kada ma a ce murjani da duwatsu masu walƙiya; farashin hikima ya fi na lu’ulu’ai.
On oubliera éclat et grandeurs; place la sagesse au-dessus de ce qu'il y a de plus intime.
19 Ba za a iya daidaita darajarta da duwatsun Tofaz na Kush ba, zallar zinariya ma ba tă isa ta saye ta ba.
On ne lui comparera pas la topaze de l'Ethiopie; on ne la pèsera pas avec de l'or pur.
20 “To, daga ina ke nan hikima ta fito? Ina fahimta take zama?
Où la sagesse a-t-elle été trouvée? En quel lieu est l'intelligence?
21 An ɓoye ta daga idanun kowane abu mai rai, har tsuntsayen sararin sama ma an ɓoye masu ita.
Elle a échappé aux recherches de tous les hommes; elle est cachée pour les oiseaux du ciel.
22 Hallaka da mutuwa suna cewa, ‘Jita-jitarta kaɗai muke ji.’
La perdition et la mort ont dit: Nous avons entendu parler de sa gloire.
23 Allah ya gane hanyar zuwa wurinta. Shi ne kaɗai ya san inda take zama,
Dieu seul a tracé sa voie; seul il sait où elle est.
24 Gama yana ganin iyakar duniya kuma yana ganin duk abin da yake ƙarƙashin sama.
Seul il voit tout sous le ciel; il connaît tout sur la terre.
25 Lokacin da ya yi iska ya sa ta hura, ya kuma auna ruwaye.
Il voit et il connaît ce qu'il a créé: la force des vents et la mesure des eaux.
26 Lokacin da ya yi wa ruwan sama doka da kuma hanya domin walƙiya,
Aux jours de la création, après avoir tout considéré, il a tout réglé jusqu'aux ébranlements du tonnerre.
27 sai ya dubi hikima ya auna ta; ya tabbatar da ita, ya gwada ta.
Alors il a vu la sagesse et il lui a montré le chemin; il l'a préparée et observée avec attention.
28 Ya kuma ce wa mutum, ‘Tsoron Ubangiji shi ne hikima, kuma guje wa mugunta shi ne fahimi.’”
Et il a dit à l'homme: Ecoute, la sagesse c'est la piété; la science c'est s'abstenir du mal.