< Ayuba 28 >

1 Akwai ramin azurfa akwai kuma wurin da ake tace zinariya.
Oui, il y a pour l’argent [un endroit] d’où on le tire, et un lieu pour l’or qu’on affine;
2 Daga cikin ƙasa ake ciro ƙarfe, ana kuma narkar da tagulla daga cikin dutse.
Le fer se tire de la poussière, et la pierre fondue donne le cuivre.
3 Mutum ya kawo ƙarshen duhu; yakan bincike zuzzurfar iyaka, yana neman duwatsu a wuri mafi duhu.
[L’homme] met fin aux ténèbres et explore jusqu’à l’extrémité de tout, la pierre d’obscurité et de l’ombre de la mort.
4 Nesa da inda mutane suke zama, yakan huda rami yă yi abin lilo, a wurin da mutane ba sa bi.
On creuse un puits loin de ceux qui séjournent [sur la terre]; oubliés du pied [de l’homme], ils sont suspendus, balancés loin des humains.
5 Cikin ƙasa inda ake samun abinci, a ƙarƙashinta kuwa zafi ne kamar wuta;
La terre, … d’elle sort le pain; et au-dessous, elle est bouleversée comme par le feu.
6 akwai duwatsu masu daraja a cikin duwatsunta, akwai kuma zinariya a cikin ƙurarta.
Ses pierres sont le lieu du saphir, et la poussière d’or s’y trouve.
7 Tsuntsu mai farauta bai san hanyarta ba, ba shahon da ya taɓa ganin ta.
C’est un sentier que l’oiseau de proie ne connaît pas, et que l’œil du vautour n’a pas aperçu;
8 Manyan namun jeji ba su taɓa binta ba, ba zakin da ya taɓa binta.
La bête fauve ne l’a pas foulé, le lion ne l’a pas traversé.
9 Hannun mutum ya iya sarrafa ƙanƙarar duwatsu, yă kuma tumɓuke tushen duwatsu.
[L’homme] porte sa main sur le roc dur, il renverse les montagnes depuis la racine;
10 Yana tona rami a cikin duwatsu idanunsa suna ganin dukan dukiyar da ke cikin duwatsun.
Il creuse des canaux dans les rochers; et son œil voit tout ce qui est précieux;
11 Yana nema daga ina ruwan rafi yake ɓulɓulowa yana kuma binciko abubuwan da suke a ɓoye yă kawo su cikin haske.
Il enserre les fleuves pour qu’ils ne suintent pas; et il produit à la lumière les choses cachées.
12 Amma a ina ne za a iya samun hikima? Ina fahimta take zama?
Mais la sagesse, où la trouvera-t-on? et où est le lieu de l’intelligence?
13 Mutum bai gane muhimmancinta ba, ba a samunta a ƙasar masu rai.
Aucun mortel n’en connaît le prix, et elle ne se trouve pas sur la terre des vivants.
14 Zurfi ya ce, “Ba ta wurina”; teku ya ce, “Ba ta wurina.”
L’abîme dit: Elle n’est pas en moi; et la mer dit: Elle n’est pas chez moi.
15 Ba irin zinariyar da za tă iya sayenta, ko kuma a iya auna nauyinta da azurfa.
Elle ne s’échange pas contre de l’or pur, et l’argent ne se pèse pas pour l’acheter.
16 Ba za a iya sayenta da zinariyar Ofir, ko sauran duwatsu masu daraja ba.
On ne la met pas dans la balance avec l’or d’Ophir, avec l’onyx précieux et le saphir.
17 Zinariya da madubi ba za su iya gwada kansu da ita ba, ba kuwa za a iya musayarta da abubuwan da aka yi da zinariya ba.
On ne peut lui comparer ni l’or ni le verre, ni l’échanger contre un vase d’or fin.
18 Kada ma a ce murjani da duwatsu masu walƙiya; farashin hikima ya fi na lu’ulu’ai.
[À côté d’elle] le corail et le cristal ne viennent pas dans la mémoire; et la possession de la sagesse vaut mieux que les perles.
19 Ba za a iya daidaita darajarta da duwatsun Tofaz na Kush ba, zallar zinariya ma ba tă isa ta saye ta ba.
La topaze d’Éthiopie ne lui est pas comparée, on ne la met pas dans la balance avec l’or pur.
20 “To, daga ina ke nan hikima ta fito? Ina fahimta take zama?
Mais la sagesse, d’où vient-elle? et où est le lieu de l’intelligence?
21 An ɓoye ta daga idanun kowane abu mai rai, har tsuntsayen sararin sama ma an ɓoye masu ita.
Elle est voilée aux yeux de tous les vivants, et elle est cachée aux oiseaux des cieux.
22 Hallaka da mutuwa suna cewa, ‘Jita-jitarta kaɗai muke ji.’
La destruction et la mort disent: De nos oreilles nous en avons entendu la rumeur.
23 Allah ya gane hanyar zuwa wurinta. Shi ne kaɗai ya san inda take zama,
Dieu comprend son chemin, et lui, il connaît son lieu.
24 Gama yana ganin iyakar duniya kuma yana ganin duk abin da yake ƙarƙashin sama.
Car lui, voit jusqu’aux bouts de la terre: sa vue s’étend sous tous les cieux.
25 Lokacin da ya yi iska ya sa ta hura, ya kuma auna ruwaye.
Quand il fixait au vent sa pesanteur, et qu’il établissait les eaux selon leur mesure;
26 Lokacin da ya yi wa ruwan sama doka da kuma hanya domin walƙiya,
Quand il faisait une loi pour la pluie, et un chemin pour le sillon de la foudre:
27 sai ya dubi hikima ya auna ta; ya tabbatar da ita, ya gwada ta.
Alors il la vit et la manifesta; il l’établit, et il la sonda aussi;
28 Ya kuma ce wa mutum, ‘Tsoron Ubangiji shi ne hikima, kuma guje wa mugunta shi ne fahimi.’”
Et il dit à l’homme: Voici, la crainte du Seigneur, c’est là la sagesse, et se retirer du mal est l’intelligence.

< Ayuba 28 >