< Ayuba 28 >
1 Akwai ramin azurfa akwai kuma wurin da ake tace zinariya.
Hopialla on hänen lähtemisensä, ja kullalla sia, jossa valetaan.
2 Daga cikin ƙasa ake ciro ƙarfe, ana kuma narkar da tagulla daga cikin dutse.
Rauta otetaan maasta, ja kivistä vaski valetaan.
3 Mutum ya kawo ƙarshen duhu; yakan bincike zuzzurfar iyaka, yana neman duwatsu a wuri mafi duhu.
Pimeydelle asetti hän lopun, ja kaiken täydellisyyden hän tutki, niin myös kiven, joka paksussa pimeydessä on, ja kuoleman varjon.
4 Nesa da inda mutane suke zama, yakan huda rami yă yi abin lilo, a wurin da mutane ba sa bi.
Siitä vuotaa senkaltainen osa, että ympäriasuvaiset ei taida siitä jalkaisin käydä ylitse: se tyhjetään ihmisiltä ja vuotaa pois.
5 Cikin ƙasa inda ake samun abinci, a ƙarƙashinta kuwa zafi ne kamar wuta;
Vilja kasvaa maasta, jonka alla se muutetaan niinkuin tuulelta.
6 akwai duwatsu masu daraja a cikin duwatsunta, akwai kuma zinariya a cikin ƙurarta.
Saphiri löydetään muutamista paikoista, ja maan kokkareita, joissa kultaa on.
7 Tsuntsu mai farauta bai san hanyarta ba, ba shahon da ya taɓa ganin ta.
Sitä polkua ei ole yksikään lintu tuntenut, eikä variksen silmä nähnyt.
8 Manyan namun jeji ba su taɓa binta ba, ba zakin da ya taɓa binta.
Ne ylpiät sikiät ei ole sitä sotkuneet, eikä jalopeura käynyt sen päällä.
9 Hannun mutum ya iya sarrafa ƙanƙarar duwatsu, yă kuma tumɓuke tushen duwatsu.
Kädellä kallioon ruvetaan, ja vuoret ylösalaisin kukistetaan.
10 Yana tona rami a cikin duwatsu idanunsa suna ganin dukan dukiyar da ke cikin duwatsun.
Ojat lasketaan kallioista, ja kaikkein kalliimmatkin näkee silmä.
11 Yana nema daga ina ruwan rafi yake ɓulɓulowa yana kuma binciko abubuwan da suke a ɓoye yă kawo su cikin haske.
Virrat estetään juoksemasta, ja ne ilmoitetaan, mitkä näissä peitetyt ovat.
12 Amma a ina ne za a iya samun hikima? Ina fahimta take zama?
Mutta kusta taito löydetään, ja kussa on ymmärryksen sia?
13 Mutum bai gane muhimmancinta ba, ba a samunta a ƙasar masu rai.
Ei yksikään ihminen tiedä hänen siaansa, eikä löydeta elävien maasta.
14 Zurfi ya ce, “Ba ta wurina”; teku ya ce, “Ba ta wurina.”
Syvyys sanoo: ei se ole minussa, ja meri sanoo: ei se ole minun tykönäni.
15 Ba irin zinariyar da za tă iya sayenta, ko kuma a iya auna nauyinta da azurfa.
Ei hänestä anneta kultaa, eikä hopiaa punnita sen hinnaksi.
16 Ba za a iya sayenta da zinariyar Ofir, ko sauran duwatsu masu daraja ba.
Ei Ophirin kulta, eli kalliit Onikin ja Saphirin kivet ole verratut hänen kanssansa.
17 Zinariya da madubi ba za su iya gwada kansu da ita ba, ba kuwa za a iya musayarta da abubuwan da aka yi da zinariya ba.
Kulta ja kallis kivi ei taideta siihen verrattaa, eikä se taideta vaihetettaa kultaisiin astioihin.
18 Kada ma a ce murjani da duwatsu masu walƙiya; farashin hikima ya fi na lu’ulu’ai.
Ramot ja Gabis ei ole mitään sen suhteen: se pidetään kalliimpana päärlyjä.
19 Ba za a iya daidaita darajarta da duwatsun Tofaz na Kush ba, zallar zinariya ma ba tă isa ta saye ta ba.
Topatsi Etiopiasta ei ole siihen verrattava, ja puhtain kulta ei maksa mitään sen suhteen.
20 “To, daga ina ke nan hikima ta fito? Ina fahimta take zama?
Kusta siis taito tulee? ja kussa on ymmärryksen sia?
21 An ɓoye ta daga idanun kowane abu mai rai, har tsuntsayen sararin sama ma an ɓoye masu ita.
Hän on peitetty kaikkein elävien silmistä, ja salattu taivaan linnuiltakin.
22 Hallaka da mutuwa suna cewa, ‘Jita-jitarta kaɗai muke ji.’
Kadotus ja kuolema sanovat: me olemme korvillamme kuulleet hänen sanomansa.
23 Allah ya gane hanyar zuwa wurinta. Shi ne kaɗai ya san inda take zama,
Jumala tietää hänen tiensä, ja hän tuntee hänen siansa.
24 Gama yana ganin iyakar duniya kuma yana ganin duk abin da yake ƙarƙashin sama.
Sillä hän katselee maan ääriin, ja näkee kaikki, mitä taivaan alla on,
25 Lokacin da ya yi iska ya sa ta hura, ya kuma auna ruwaye.
Niin että hän antaa tuulelle hänen painonsa ja vedelle hänen mittansa.
26 Lokacin da ya yi wa ruwan sama doka da kuma hanya domin walƙiya,
Koska hän asetti sateelle määrän ja pitkäisen tulen leimauksille hänen tiensä,
27 sai ya dubi hikima ya auna ta; ya tabbatar da ita, ya gwada ta.
Silloin näki hän sen ja luki sen: hän valmisti sen ja myös tutki sen,
28 Ya kuma ce wa mutum, ‘Tsoron Ubangiji shi ne hikima, kuma guje wa mugunta shi ne fahimi.’”
Ja sanoi ihmiselle: katso, Herran pelko on taito; ja karttaa pahaa on ymmärrys.