< Ayuba 28 >
1 Akwai ramin azurfa akwai kuma wurin da ake tace zinariya.
“Surely there is a mine for silver and a place where gold is refined.
2 Daga cikin ƙasa ake ciro ƙarfe, ana kuma narkar da tagulla daga cikin dutse.
Iron is taken from the earth, and copper is smelted from ore.
3 Mutum ya kawo ƙarshen duhu; yakan bincike zuzzurfar iyaka, yana neman duwatsu a wuri mafi duhu.
Man puts an end to the darkness; he probes the farthest recesses for ore in deepest darkness.
4 Nesa da inda mutane suke zama, yakan huda rami yă yi abin lilo, a wurin da mutane ba sa bi.
Far from human habitation he cuts a shaft in places forgotten by the foot of man. Far from men he dangles and sways.
5 Cikin ƙasa inda ake samun abinci, a ƙarƙashinta kuwa zafi ne kamar wuta;
Food may come from the earth, but from below it is transformed as by fire.
6 akwai duwatsu masu daraja a cikin duwatsunta, akwai kuma zinariya a cikin ƙurarta.
Its rocks are the source of sapphires, containing flecks of gold.
7 Tsuntsu mai farauta bai san hanyarta ba, ba shahon da ya taɓa ganin ta.
No bird of prey knows that path; no falcon’s eye has seen it.
8 Manyan namun jeji ba su taɓa binta ba, ba zakin da ya taɓa binta.
Proud beasts have never trodden it; no lion has ever prowled over it.
9 Hannun mutum ya iya sarrafa ƙanƙarar duwatsu, yă kuma tumɓuke tushen duwatsu.
The miner strikes the flint; he overturns mountains at their base.
10 Yana tona rami a cikin duwatsu idanunsa suna ganin dukan dukiyar da ke cikin duwatsun.
He hews out channels in the rocks, and his eyes spot every treasure.
11 Yana nema daga ina ruwan rafi yake ɓulɓulowa yana kuma binciko abubuwan da suke a ɓoye yă kawo su cikin haske.
He stops up the sources of the streams to bring what is hidden to light.
12 Amma a ina ne za a iya samun hikima? Ina fahimta take zama?
But where can wisdom be found, and where does understanding dwell?
13 Mutum bai gane muhimmancinta ba, ba a samunta a ƙasar masu rai.
No man can know its value, nor is it found in the land of the living.
14 Zurfi ya ce, “Ba ta wurina”; teku ya ce, “Ba ta wurina.”
The ocean depths say, ‘It is not in me,’ while the sea declares, ‘It is not with me.’
15 Ba irin zinariyar da za tă iya sayenta, ko kuma a iya auna nauyinta da azurfa.
It cannot be bought with gold, nor can its price be weighed out in silver.
16 Ba za a iya sayenta da zinariyar Ofir, ko sauran duwatsu masu daraja ba.
It cannot be valued in the gold of Ophir, in precious onyx or sapphire.
17 Zinariya da madubi ba za su iya gwada kansu da ita ba, ba kuwa za a iya musayarta da abubuwan da aka yi da zinariya ba.
Neither gold nor crystal can compare to it, nor jewels of fine gold be exchanged for it.
18 Kada ma a ce murjani da duwatsu masu walƙiya; farashin hikima ya fi na lu’ulu’ai.
Coral and quartz are unworthy of mention; the price of wisdom is beyond rubies.
19 Ba za a iya daidaita darajarta da duwatsun Tofaz na Kush ba, zallar zinariya ma ba tă isa ta saye ta ba.
Topaz from Cush cannot compare to it, nor can it be valued in pure gold.
20 “To, daga ina ke nan hikima ta fito? Ina fahimta take zama?
From where then does wisdom come, and where does understanding dwell?
21 An ɓoye ta daga idanun kowane abu mai rai, har tsuntsayen sararin sama ma an ɓoye masu ita.
It is hidden from the eyes of every living thing and concealed from the birds of the air.
22 Hallaka da mutuwa suna cewa, ‘Jita-jitarta kaɗai muke ji.’
Abaddon and Death say, ‘We have heard a rumor about it.’
23 Allah ya gane hanyar zuwa wurinta. Shi ne kaɗai ya san inda take zama,
But God understands its way, and He knows its place.
24 Gama yana ganin iyakar duniya kuma yana ganin duk abin da yake ƙarƙashin sama.
For He looks to the ends of the earth and sees everything under the heavens.
25 Lokacin da ya yi iska ya sa ta hura, ya kuma auna ruwaye.
When God fixed the weight of the wind and measured out the waters,
26 Lokacin da ya yi wa ruwan sama doka da kuma hanya domin walƙiya,
when He set a limit for the rain and a path for the thunderbolt,
27 sai ya dubi hikima ya auna ta; ya tabbatar da ita, ya gwada ta.
then He looked at wisdom and appraised it; He established it and searched it out.
28 Ya kuma ce wa mutum, ‘Tsoron Ubangiji shi ne hikima, kuma guje wa mugunta shi ne fahimi.’”
And He said to man, ‘Behold, the fear of the Lord, that is wisdom, and to turn away from evil is understanding.’”