< Ayuba 28 >
1 Akwai ramin azurfa akwai kuma wurin da ake tace zinariya.
Zeker, er is een plaats, waaruit het zilver komt, Een oord, waar het goud wordt gewassen,
2 Daga cikin ƙasa ake ciro ƙarfe, ana kuma narkar da tagulla daga cikin dutse.
Het ijzer uit de bodem gehaald, De steen tot koper gesmolten;
3 Mutum ya kawo ƙarshen duhu; yakan bincike zuzzurfar iyaka, yana neman duwatsu a wuri mafi duhu.
Waar men in de uiterste duisternis doordringt, En de diepste plekken doorvorst. In de rotsen, duister en somber.
4 Nesa da inda mutane suke zama, yakan huda rami yă yi abin lilo, a wurin da mutane ba sa bi.
Worden schachten gehakt door een volk, dat er niet hoort, Dat door de wandelaars wordt vergeten, Daar ver van de mensen hangt en zweeft;
5 Cikin ƙasa inda ake samun abinci, a ƙarƙashinta kuwa zafi ne kamar wuta;
En de aarde, waaruit het brood ontspruit, Wordt in haar ingewanden omgewoeld als door vuur.
6 akwai duwatsu masu daraja a cikin duwatsunta, akwai kuma zinariya a cikin ƙurarta.
Haar rotsen zijn de plaats van saffier, Haar stof bevat goud;
7 Tsuntsu mai farauta bai san hanyarta ba, ba shahon da ya taɓa ganin ta.
De arend kent er de weg niet heen, Het valkenoog bespeurt hem niet;
8 Manyan namun jeji ba su taɓa binta ba, ba zakin da ya taɓa binta.
De roofdieren betreden hem niet, De luipaard gaat er niet heen.
9 Hannun mutum ya iya sarrafa ƙanƙarar duwatsu, yă kuma tumɓuke tushen duwatsu.
De mens slaat zijn hand aan de harde steen, Woelt de bergen om van hun grondslag af,
10 Yana tona rami a cikin duwatsu idanunsa suna ganin dukan dukiyar da ke cikin duwatsun.
Breekt gangen in de rotsen uit, Niets kostbaars ontsnapt aan zijn oog;
11 Yana nema daga ina ruwan rafi yake ɓulɓulowa yana kuma binciko abubuwan da suke a ɓoye yă kawo su cikin haske.
Hij zoekt de bronnen der stromen af, En brengt wat verborgen lag aan het licht.
12 Amma a ina ne za a iya samun hikima? Ina fahimta take zama?
Maar de wijsheid, waar is zij te vinden, En waar is het oord van het inzicht?
13 Mutum bai gane muhimmancinta ba, ba a samunta a ƙasar masu rai.
De mens kent er de weg niet heen, In het land der levenden bevindt ze zich niet.
14 Zurfi ya ce, “Ba ta wurina”; teku ya ce, “Ba ta wurina.”
De afgrond roept: In mij is ze niet! De zee herhaalt: Ze is niet bij mij!
15 Ba irin zinariyar da za tă iya sayenta, ko kuma a iya auna nauyinta da azurfa.
Zij wordt niet gekocht voor het fijnste goud, Geen zilver gewogen, om haar te betalen;
16 Ba za a iya sayenta da zinariyar Ofir, ko sauran duwatsu masu daraja ba.
Zij wordt niet geschat tegen goud van Ofir, Tegen kostbare onyx, noch saffier;
17 Zinariya da madubi ba za su iya gwada kansu da ita ba, ba kuwa za a iya musayarta da abubuwan da aka yi da zinariya ba.
Geen goud, geen glaswerk kan haar evenaren, Geen gouden vaas is haar prijs.
18 Kada ma a ce murjani da duwatsu masu walƙiya; farashin hikima ya fi na lu’ulu’ai.
Paarlen en kristal zijn naast haar niet in tel, Het vinden der wijsheid gaat dat van koralen te boven;
19 Ba za a iya daidaita darajarta da duwatsun Tofaz na Kush ba, zallar zinariya ma ba tă isa ta saye ta ba.
Topaas van Koesj kan het niet bij haar halen, Het zuiverst goud weegt niet tegen haar op.
20 “To, daga ina ke nan hikima ta fito? Ina fahimta take zama?
De wijsheid, waar komt zij vandaan; Het inzicht, waar is zijn plaats?
21 An ɓoye ta daga idanun kowane abu mai rai, har tsuntsayen sararin sama ma an ɓoye masu ita.
Zij ligt verborgen voor het oog van al wat leeft, Verscholen voor de vogels in de lucht;
22 Hallaka da mutuwa suna cewa, ‘Jita-jitarta kaɗai muke ji.’
De onderwereld en dood roepen uit: Onze oren hebben enkel van haar bij geruchte gehoord.
23 Allah ya gane hanyar zuwa wurinta. Shi ne kaɗai ya san inda take zama,
Het is God, die de weg naar haar kent, Hij alleen weet, waar zij toeft.
24 Gama yana ganin iyakar duniya kuma yana ganin duk abin da yake ƙarƙashin sama.
Want Hij blikte tot aan de grenzen der aarde, Zag al wat onder de hemel bestond:
25 Lokacin da ya yi iska ya sa ta hura, ya kuma auna ruwaye.
Toen Hij het gewicht van de wind bepaalde, De maat voor het water bestemde;
26 Lokacin da ya yi wa ruwan sama doka da kuma hanya domin walƙiya,
Toen Hij de regen zijn wet gaf, En de donder zijn weg.
27 sai ya dubi hikima ya auna ta; ya tabbatar da ita, ya gwada ta.
Toen aanschouwde Hij haar en verkondigde haar, Kende Hij haar en doorgrondde haar;
28 Ya kuma ce wa mutum, ‘Tsoron Ubangiji shi ne hikima, kuma guje wa mugunta shi ne fahimi.’”
Maar Hij sprak tot den mens: Zie, de vreze des Heren is wijsheid, En het kwade te mijden is inzicht!