< Ayuba 27 >

1 Ayuba kuwa ya ci gaba da magana,
Eyüp anlatmaya devam etti:
2 “Na rantse da Allah mai rai, wanda ya danne mini gaskiyata, Maɗaukaki, wanda ya sa nake cikin ɗacin rai.
“Hakkımı elimden alan Tanrı'nın varlığı hakkı için, Bana acı çektiren Her Şeye Gücü Yeten'in hakkı için,
3 Muddin ina da rai a cikina kuma numfashin Allah yana cikin hancina,
İçimde yaşam belirtisi olduğu sürece, Tanrı'nın soluğu burnumda olduğu sürece,
4 bakina ba zai faɗi mugun abu ba, harshena kuma ba zai yi ƙarya ba.
Ağzımdan kötü söz çıkmayacak, Dilimden yalan dökülmeyecek.
5 Ba zan taɓa yarda cewa kuna da gaskiya ba; har in mutu, ba zan daina kāre mutuncina ba.
Size asla hak vermeyecek, Son soluğumu verene dek suçsuz olduğumu söyleyeceğim.
6 Zan ci gaba da adalcina, ba zan fasa ba; lamirina ba zai taɓa yashe ni ba, dukan kwanakin raina.
Doğruluğuma sarılacak, onu bırakmayacağım, Yaşadığım sürece vicdanım beni suçlamayacak.
7 “Bari maƙiyana su zama kamar mugaye, masu gāba da ni kuma su zama kamar marasa adalci.
“Düşmanlarım kötüler gibi, Bana saldıranlar haksızlar gibi cezalandırılsın.
8 Gama wane bege marar tsoron Allah yake da shi, lokacin da aka datse shi, lokacin da Allah ya ɗauke ransa?
Tanrısız insanın umudu nedir Tanrı onu yok ettiğinde, canını aldığında?
9 Ko Allah yana sauraron kukansa lokacin da ƙunci ya auko masa?
Başına sıkıntı geldiğinde, Tanrı feryadını duyar mı?
10 Ko zai sami farin ciki daga Maɗaukaki? Ko zai yi kira ga Allah a kowane lokaci?
Her Şeye Gücü Yeten'den zevk alır mı? Her zaman Tanrı'ya yakarır mı?
11 “Zan koya muku game da ikon Allah; ba zan ɓoye hanyoyin Maɗaukaki ba.
“Tanrı'nın gücünü size öğreteceğim, Her Şeye Gücü Yeten'in tasarısını gizlemeyeceğim.
12 Duk kun ga wannan ku da kanku saboda haka me ya sa kuke maganganun nan marasa ma’ana?
Aslında siz, hepiniz gördünüz bunu, Öyleyse ne diye boş boş konuşuyorsunuz?
13 “Ga abin da mugaye za su samu gādon da azzalumi zai samu daga Maɗaukaki.
“Kötünün Tanrı'dan alacağı pay, Zorbanın Her Şeye Gücü Yeten'den alacağı miras şudur:
14 Kome yawan’ya’yansa, takobi za tă gama da su; zuriyarsa ba za su taɓa samun isashen abinci ba.
Çocukları ne kadar çok olursa olsun, kılıçla öldürülecek, Soyu yeterince ekmek bulamayacaktır.
15 Waɗanda suka tsira annoba za tă kashe su, kuma gwaurayensu ba za su yi kukan mutuwarsu ba.
Sağ kalanlar hastalıktan ölüp gömülecek, Dul karıları ağlamayacaktır.
16 Ko da yake ya tara azurfa kamar ƙasa, tufafi kuma kamar tarin ƙasa,
Kötü insan kum gibi gümüş yığsa, Yığınla giysi biriktirse,
17 abin da ya tara masu adalci za su sa marasa laifi za su raba azurfarsa.
Onun biriktirdiğini doğru insan giyecek, Gümüşü suçsuz paylaşacak.
18 Gidan da ya gina kamar gidan gizo-gizo, kamar bukkar mai tsaro.
Evini güve kozası gibi inşa eder, Bekçinin kurduğu çardak gibi.
19 Attajiri zai kwanta, amma daga wannan shi ke nan; lokacin da zai buɗe idanunsa, kome ya tafi.
Zengin olarak yatar, ama bu öyle sürmez, Gözlerini açtığında hepsi yok olup gitmiştir.
20 Tsoro zai kwashe shi kamar ambaliyar ruwa; Da dare iska za tă tafi da shi.
Dehşet onu sel gibi basar, Kasırga gece kapar götürür.
21 Iskar gabas za tă tafi da shi; shi ke nan ya ƙare; za tă share shi daga wurinsa.
Doğu rüzgarı onu uçurup götürür, Yerinden silip süpürür.
22 Za tă murɗe shi ba tausayi, lokacin da yake guje wa ikon iskar.
Acımasızca üzerine eser, Elinden kaçmaya çalışırken.
23 Zai tafa hannu yă yi tsaki yă kawar da shi daga wurinsa.”
Onunla alay ederek el çırpar, Yerinden ıslık çalar.”

< Ayuba 27 >