< Ayuba 27 >
1 Ayuba kuwa ya ci gaba da magana,
Y tornó Job a tomar su parábola, y dijo:
2 “Na rantse da Allah mai rai, wanda ya danne mini gaskiyata, Maɗaukaki, wanda ya sa nake cikin ɗacin rai.
Vive el Dios que me quitó mi derecho; y el Omnipotente, que amargó mi alma:
3 Muddin ina da rai a cikina kuma numfashin Allah yana cikin hancina,
Que todo el tiempo que mi alma estuviere en mí, y hubiere resuello de Dios en mis narices,
4 bakina ba zai faɗi mugun abu ba, harshena kuma ba zai yi ƙarya ba.
Mis labios no hablarán iniquidad: ni mi lengua pronunciará engaño.
5 Ba zan taɓa yarda cewa kuna da gaskiya ba; har in mutu, ba zan daina kāre mutuncina ba.
Nunca tal me acontezca, que yo os justifique: hasta morir no quitaré mi integridad de mí.
6 Zan ci gaba da adalcina, ba zan fasa ba; lamirina ba zai taɓa yashe ni ba, dukan kwanakin raina.
Mi justicia tengo asida, y no la aflojaré, no se avergonzará mi corazón de mis días.
7 “Bari maƙiyana su zama kamar mugaye, masu gāba da ni kuma su zama kamar marasa adalci.
Sea como el impío mi enemigo, y como el inicuo mi adversario.
8 Gama wane bege marar tsoron Allah yake da shi, lokacin da aka datse shi, lokacin da Allah ya ɗauke ransa?
Porque ¿qué es la esperanza del hipócrita, si mucho hubiere robado, cuando Dios arrebatare su alma?
9 Ko Allah yana sauraron kukansa lokacin da ƙunci ya auko masa?
¿Oirá Dios su clamor, cuando viniere sobre él la tribulación?
10 Ko zai sami farin ciki daga Maɗaukaki? Ko zai yi kira ga Allah a kowane lokaci?
¿Se deleitará en el Omnipotente? ¿llamará a Dios en todo tiempo?
11 “Zan koya muku game da ikon Allah; ba zan ɓoye hanyoyin Maɗaukaki ba.
Yo os enseñaré lo que está en la mano de Dios: no esconderé lo que está acerca del Omnipotente.
12 Duk kun ga wannan ku da kanku saboda haka me ya sa kuke maganganun nan marasa ma’ana?
He aquí, que todos vosotros lo habéis visto: ¿por qué pues os desvanecéis con vanidad?
13 “Ga abin da mugaye za su samu gādon da azzalumi zai samu daga Maɗaukaki.
Esta es la suerte del hombre impío acerca de Dios, y la herencia que los violentos han de recibir del Omnipotente.
14 Kome yawan’ya’yansa, takobi za tă gama da su; zuriyarsa ba za su taɓa samun isashen abinci ba.
Si sus hijos fueren multiplicados, serán para la espada, y sus pequeños no se hartarán de pan.
15 Waɗanda suka tsira annoba za tă kashe su, kuma gwaurayensu ba za su yi kukan mutuwarsu ba.
Los que de ellos quedaren, en muerte serán sepultados, y sus viudas no llorarán.
16 Ko da yake ya tara azurfa kamar ƙasa, tufafi kuma kamar tarin ƙasa,
Sí amontonare plata como polvo, y si aparejare ropa como lodo:
17 abin da ya tara masu adalci za su sa marasa laifi za su raba azurfarsa.
Aparejará, mas el justo se vestirá, y el inocente repartirá la plata.
18 Gidan da ya gina kamar gidan gizo-gizo, kamar bukkar mai tsaro.
Edificó su casa como la polilla, y como cabaña que hizo alguna guarda.
19 Attajiri zai kwanta, amma daga wannan shi ke nan; lokacin da zai buɗe idanunsa, kome ya tafi.
El rico dormirá, mas no será recogido: abrirá sus ojos, y no verá a nadie.
20 Tsoro zai kwashe shi kamar ambaliyar ruwa; Da dare iska za tă tafi da shi.
Asirán de él terrores como aguas: torbellino le arrebatará de noche.
21 Iskar gabas za tă tafi da shi; shi ke nan ya ƙare; za tă share shi daga wurinsa.
Tomarle ha solano, e irse ha: y tempestad le arrebatará de su lugar.
22 Za tă murɗe shi ba tausayi, lokacin da yake guje wa ikon iskar.
Y echará sobre él, y no perdonará: huyendo huirá de su mano.
23 Zai tafa hannu yă yi tsaki yă kawar da shi daga wurinsa.”
Batirá sus manos sobre él, y desde su lugar le silbará.