< Ayuba 27 >
1 Ayuba kuwa ya ci gaba da magana,
Job comenzó a hablar de nuevo.
2 “Na rantse da Allah mai rai, wanda ya danne mini gaskiyata, Maɗaukaki, wanda ya sa nake cikin ɗacin rai.
“Les prometo que, mientras viva Dios, que me ha negado la justicia; el Todopoderoso, que me ha amargado la vida,
3 Muddin ina da rai a cikina kuma numfashin Allah yana cikin hancina,
mientras tenga vida, mientras el aliento de Dios permanezca en mis fosas nasales,
4 bakina ba zai faɗi mugun abu ba, harshena kuma ba zai yi ƙarya ba.
mis labios nunca dirán mentiras, mi lengua nunca será deshonesta.
5 Ba zan taɓa yarda cewa kuna da gaskiya ba; har in mutu, ba zan daina kāre mutuncina ba.
Nunca aceptaré que tengan la razón; insistiré en mi inocencia hasta el día de mi muerte.
6 Zan ci gaba da adalcina, ba zan fasa ba; lamirina ba zai taɓa yashe ni ba, dukan kwanakin raina.
Estoy convencido de que tengo razón y nunca dejaré de creerlo; mi conciencia no me condenará mientras viva.
7 “Bari maƙiyana su zama kamar mugaye, masu gāba da ni kuma su zama kamar marasa adalci.
“Que mi enemigo se vuelva como los malvados; que los que se oponen a mí se vuelvan como los que hacen el mal.
8 Gama wane bege marar tsoron Allah yake da shi, lokacin da aka datse shi, lokacin da Allah ya ɗauke ransa?
Porque, ¿qué esperanza tienen los que rechazan a Dios, cuando él los derribe, cuando Dios ponga fin a sus vidas?
9 Ko Allah yana sauraron kukansa lokacin da ƙunci ya auko masa?
Cuando les lleguen tiempos de angustia, ¿escuchará Dios su grito de auxilio?
10 Ko zai sami farin ciki daga Maɗaukaki? Ko zai yi kira ga Allah a kowane lokaci?
¿Tienen una buena relación con el Todopoderoso? ¿Pueden invocar a Dios en cualquier momento?
11 “Zan koya muku game da ikon Allah; ba zan ɓoye hanyoyin Maɗaukaki ba.
Permítanme explicarles el poder de Dios. No voy a retener nada de lo que el Todopoderoso ha planeado.
12 Duk kun ga wannan ku da kanku saboda haka me ya sa kuke maganganun nan marasa ma’ana?
Si todos ustedes han reconocido esto, ¿por qué hablan de tonterías tan vanas?
13 “Ga abin da mugaye za su samu gādon da azzalumi zai samu daga Maɗaukaki.
“Esto es lo que Dios dispone como destino para los malvados, esta es la herencia que los despiadados recibirán del Todopoderoso,
14 Kome yawan’ya’yansa, takobi za tă gama da su; zuriyarsa ba za su taɓa samun isashen abinci ba.
aunque tengan muchos hijos, experimentarán muertes violentas o morirán de hambre.
15 Waɗanda suka tsira annoba za tă kashe su, kuma gwaurayensu ba za su yi kukan mutuwarsu ba.
Los que sobrevivan morirán de enfermedad, y ni siquiera sus viudas se lamentarán por ellos.
16 Ko da yake ya tara azurfa kamar ƙasa, tufafi kuma kamar tarin ƙasa,
Aunque amontonen plata como polvo y ropa como montones de barro,
17 abin da ya tara masu adalci za su sa marasa laifi za su raba azurfarsa.
los que hacen el bien se pondrán la ropa y los inocentes se repartirán la plata.
18 Gidan da ya gina kamar gidan gizo-gizo, kamar bukkar mai tsaro.
Construyen sus casas como la polilla; como un endeble refugio hecho por un vigilante.
19 Attajiri zai kwanta, amma daga wannan shi ke nan; lokacin da zai buɗe idanunsa, kome ya tafi.
Se acuestan ricos, pero nunca más. Porque cuando se despiertan, todo ha desaparecido.
20 Tsoro zai kwashe shi kamar ambaliyar ruwa; Da dare iska za tă tafi da shi.
Olas de pánico los inundan; en la noche un torbellino los arrebata.
21 Iskar gabas za tă tafi da shi; shi ke nan ya ƙare; za tă share shi daga wurinsa.
El viento del este los levanta y se van, llevados lejos de donde estaban.
22 Za tă murɗe shi ba tausayi, lokacin da yake guje wa ikon iskar.
El viento los golpea con toda su fuerza; intentan escapar desesperadamente.
23 Zai tafa hannu yă yi tsaki yă kawar da shi daga wurinsa.”
Las personas aplaudirles y sisearles allí donde estén”.