< Ayuba 27 >

1 Ayuba kuwa ya ci gaba da magana,
Addidit quoque Job, assumens parabolam suam, et dixit:
2 “Na rantse da Allah mai rai, wanda ya danne mini gaskiyata, Maɗaukaki, wanda ya sa nake cikin ɗacin rai.
[Vivit Deus, qui abstulit judicium meum, et Omnipotens, qui ad amaritudinem adduxit animam meam.
3 Muddin ina da rai a cikina kuma numfashin Allah yana cikin hancina,
Quia donec superest halitus in me, et spiritus Dei in naribus meis,
4 bakina ba zai faɗi mugun abu ba, harshena kuma ba zai yi ƙarya ba.
non loquentur labia mea iniquitatem, nec lingua mea meditabitur mendacium.
5 Ba zan taɓa yarda cewa kuna da gaskiya ba; har in mutu, ba zan daina kāre mutuncina ba.
Absit a me ut justos vos esse judicem: donec deficiam, non recedam ab innocentia mea.
6 Zan ci gaba da adalcina, ba zan fasa ba; lamirina ba zai taɓa yashe ni ba, dukan kwanakin raina.
Justificationem meam, quam cœpi tenere, non deseram: neque enim reprehendit me cor meum in omni vita mea.
7 “Bari maƙiyana su zama kamar mugaye, masu gāba da ni kuma su zama kamar marasa adalci.
Sit ut impius, inimicus meus, et adversarius meus quasi iniquus.
8 Gama wane bege marar tsoron Allah yake da shi, lokacin da aka datse shi, lokacin da Allah ya ɗauke ransa?
Quæ est enim spes hypocritæ, si avare rapiat, et non liberet Deus animam ejus?
9 Ko Allah yana sauraron kukansa lokacin da ƙunci ya auko masa?
Numquid Deus audiet clamorem ejus, cum venerit super eum angustia?
10 Ko zai sami farin ciki daga Maɗaukaki? Ko zai yi kira ga Allah a kowane lokaci?
aut poterit in Omnipotente delectari, et invocare Deum omni tempore?
11 “Zan koya muku game da ikon Allah; ba zan ɓoye hanyoyin Maɗaukaki ba.
Docebo vos per manum Dei quæ Omnipotens habeat, nec abscondam.
12 Duk kun ga wannan ku da kanku saboda haka me ya sa kuke maganganun nan marasa ma’ana?
Ecce vos omnes nostis: et quid sine causa vana loquimini?
13 “Ga abin da mugaye za su samu gādon da azzalumi zai samu daga Maɗaukaki.
Hæc est pars hominis impii apud Deum, et hæreditas violentorum, quam ob Omnipotente suscipient.
14 Kome yawan’ya’yansa, takobi za tă gama da su; zuriyarsa ba za su taɓa samun isashen abinci ba.
Si multiplicati fuerint filii ejus, in gladio erunt, et nepotes ejus non saturabuntur pane:
15 Waɗanda suka tsira annoba za tă kashe su, kuma gwaurayensu ba za su yi kukan mutuwarsu ba.
qui reliqui fuerint ex eo sepelientur in interitu, et viduæ illius non plorabunt.
16 Ko da yake ya tara azurfa kamar ƙasa, tufafi kuma kamar tarin ƙasa,
Si comportaverit quasi terram argentum, et sicut lutum præparaverit vestimenta:
17 abin da ya tara masu adalci za su sa marasa laifi za su raba azurfarsa.
præparabit quidem, sed justus vestietur illis, et argentum innocens dividet.
18 Gidan da ya gina kamar gidan gizo-gizo, kamar bukkar mai tsaro.
Ædificavit sicut tinea domum suam, et sicut custos fecit umbraculum.
19 Attajiri zai kwanta, amma daga wannan shi ke nan; lokacin da zai buɗe idanunsa, kome ya tafi.
Dives, cum dormierit, nihil secum auferet: aperiet oculos suos, et nihil inveniet.
20 Tsoro zai kwashe shi kamar ambaliyar ruwa; Da dare iska za tă tafi da shi.
Apprehendet eum quasi aqua inopia: nocte opprimet eum tempestas.
21 Iskar gabas za tă tafi da shi; shi ke nan ya ƙare; za tă share shi daga wurinsa.
Tollet eum ventus urens, et auferet, et velut turbo rapiet eum de loco suo.
22 Za tă murɗe shi ba tausayi, lokacin da yake guje wa ikon iskar.
Et mittet super eum, et non parcet: de manu ejus fugiens fugiet.
23 Zai tafa hannu yă yi tsaki yă kawar da shi daga wurinsa.”
Stringet super eum manus suas, et sibilabit super illum, intuens locum ejus.]

< Ayuba 27 >