< Ayuba 27 >

1 Ayuba kuwa ya ci gaba da magana,
ヨブまた語を繼ていはく
2 “Na rantse da Allah mai rai, wanda ya danne mini gaskiyata, Maɗaukaki, wanda ya sa nake cikin ɗacin rai.
われに義しき審判を施したまはざる神 わが心魂をなやまし給ふ全能者 此神は活く
3 Muddin ina da rai a cikina kuma numfashin Allah yana cikin hancina,
(わが生命なほ全くわれの衷にあり 神の氣息なほわが鼻にあり)
4 bakina ba zai faɗi mugun abu ba, harshena kuma ba zai yi ƙarya ba.
わが口は惡を言ず わが舌は謊言を語らじ
5 Ba zan taɓa yarda cewa kuna da gaskiya ba; har in mutu, ba zan daina kāre mutuncina ba.
我決めて汝等を是とせじ 我に死るまで我が罪なきを言ことを息じ
6 Zan ci gaba da adalcina, ba zan fasa ba; lamirina ba zai taɓa yashe ni ba, dukan kwanakin raina.
われ堅くわが正義を持ちて之を棄じ 我は今まで一日も心に責られし事なし
7 “Bari maƙiyana su zama kamar mugaye, masu gāba da ni kuma su zama kamar marasa adalci.
我に敵する者は惡き者と成り我を攻る者は義からざる者と成るべし
8 Gama wane bege marar tsoron Allah yake da shi, lokacin da aka datse shi, lokacin da Allah ya ɗauke ransa?
邪曲なる者もし神に絶れその魂神を脱とらるるに於ては何の望かあらん
9 Ko Allah yana sauraron kukansa lokacin da ƙunci ya auko masa?
かれ艱難に罹る時に神その呼號を聽いれたまはんや
10 Ko zai sami farin ciki daga Maɗaukaki? Ko zai yi kira ga Allah a kowane lokaci?
かれ全能者を喜こばんや 常に神を龥んや
11 “Zan koya muku game da ikon Allah; ba zan ɓoye hanyoyin Maɗaukaki ba.
われ神の御手を汝等に教へん 全能者の道を汝等に隱さじ
12 Duk kun ga wannan ku da kanku saboda haka me ya sa kuke maganganun nan marasa ma’ana?
視よ汝等もみな自らこれを觀たり 然るに何ぞ斯愚蒙をきはむるや
13 “Ga abin da mugaye za su samu gādon da azzalumi zai samu daga Maɗaukaki.
惡き人の神に得る分 強暴の人の全能者より受る業は是なり
14 Kome yawan’ya’yansa, takobi za tă gama da su; zuriyarsa ba za su taɓa samun isashen abinci ba.
その子等蕃れば劍に殺さる その子孫は食物に飽ず
15 Waɗanda suka tsira annoba za tă kashe su, kuma gwaurayensu ba za su yi kukan mutuwarsu ba.
その遺れる者は疫病に斃れて埋められ その妻等は哀哭をなさず
16 Ko da yake ya tara azurfa kamar ƙasa, tufafi kuma kamar tarin ƙasa,
かれ銀を積むこと塵のごとく衣服を備ふること土のごとくなるとも
17 abin da ya tara masu adalci za su sa marasa laifi za su raba azurfarsa.
その備ふる者は義き人これを着ん またその銀は無辜者これを分ち取ん
18 Gidan da ya gina kamar gidan gizo-gizo, kamar bukkar mai tsaro.
その建る家は蟲の巣のごとく また番人の造る茅家のごとし
19 Attajiri zai kwanta, amma daga wannan shi ke nan; lokacin da zai buɗe idanunsa, kome ya tafi.
彼は富る身にて寢臥し重ねて興ること無し また目を開けば即ちその身きえ亡す
20 Tsoro zai kwashe shi kamar ambaliyar ruwa; Da dare iska za tă tafi da shi.
懼ろしき事大水のごとく彼に追及き 夜の暴風かれを奪ひ去る
21 Iskar gabas za tă tafi da shi; shi ke nan ya ƙare; za tă share shi daga wurinsa.
東風かれを颺げて去り 彼をその處より吹はらふ
22 Za tă murɗe shi ba tausayi, lokacin da yake guje wa ikon iskar.
神かれを射て恤まず 彼その手より逃れんともがく
23 Zai tafa hannu yă yi tsaki yă kawar da shi daga wurinsa.”
人かれに對ひて手を鳴し嘲りわらひてその處をいでゆかしむ

< Ayuba 27 >