< Ayuba 27 >
1 Ayuba kuwa ya ci gaba da magana,
Et Job continuant à parler en discours relevés, dit:
2 “Na rantse da Allah mai rai, wanda ya danne mini gaskiyata, Maɗaukaki, wanda ya sa nake cikin ɗacin rai.
Par le Dieu vivant qui me prive de mon droit, et par le Tout-puissant qui a mis l'amertume dans mon âme,
3 Muddin ina da rai a cikina kuma numfashin Allah yana cikin hancina,
(car je ne perds pas haleine encore, et j'ai toujours dans mes narines le souffle de Dieu)
4 bakina ba zai faɗi mugun abu ba, harshena kuma ba zai yi ƙarya ba.
non! mes lèvres ne calomnieront pas, et ma langue ne dira rien de faux.
5 Ba zan taɓa yarda cewa kuna da gaskiya ba; har in mutu, ba zan daina kāre mutuncina ba.
Loin de moi la pensée de vous donner raison! Jusqu'à mon dernier soupir, je ne me laisserai pas ravir mon innocence;
6 Zan ci gaba da adalcina, ba zan fasa ba; lamirina ba zai taɓa yashe ni ba, dukan kwanakin raina.
je tiens à ma justice, et je n'y renoncerai point; mon cœur ne me reproche aucun de mes jours.
7 “Bari maƙiyana su zama kamar mugaye, masu gāba da ni kuma su zama kamar marasa adalci.
Que mon ennemi soit tel que l'impie, et mon adversaire semblable au méchant!
8 Gama wane bege marar tsoron Allah yake da shi, lokacin da aka datse shi, lokacin da Allah ya ɗauke ransa?
Eh! quel espoir a l'impie, quand Dieu tranche, quand Il lui arrache sa vie?
9 Ko Allah yana sauraron kukansa lokacin da ƙunci ya auko masa?
Dieu écoute-t-Il les cris qu'il pousse, quand l'angoisse l'assaille?
10 Ko zai sami farin ciki daga Maɗaukaki? Ko zai yi kira ga Allah a kowane lokaci?
Est-ce dans le Tout-puissant qu'il cherche sa joie? Est-ce Dieu qu'il invoque dans tous les moments?
11 “Zan koya muku game da ikon Allah; ba zan ɓoye hanyoyin Maɗaukaki ba.
Je veux vous montrer comment agit Dieu, ne pas vous celer la pensée du Tout-puissant.
12 Duk kun ga wannan ku da kanku saboda haka me ya sa kuke maganganun nan marasa ma’ana?
Je l'accorde, vous avez bien observé! mais pourquoi tirez-vous une conclusion vaine?
13 “Ga abin da mugaye za su samu gādon da azzalumi zai samu daga Maɗaukaki.
Tel est bien le lot que Dieu donne à l'impie, et la part que le méchant obtient du Tout-puissant:
14 Kome yawan’ya’yansa, takobi za tă gama da su; zuriyarsa ba za su taɓa samun isashen abinci ba.
s'il a nombre de fils, c'est une proie pour l'épée, et ses rejetons n'ont pas de pain à manger;
15 Waɗanda suka tsira annoba za tă kashe su, kuma gwaurayensu ba za su yi kukan mutuwarsu ba.
ceux qui restent de lui, sont conduits par la mort au tombeau, et leurs veuves ne pleurent point;
16 Ko da yake ya tara azurfa kamar ƙasa, tufafi kuma kamar tarin ƙasa,
qu'il entasse l'argent comme la poussière, qu'il se procure un riche vestiaire,
17 abin da ya tara masu adalci za su sa marasa laifi za su raba azurfarsa.
il l'acquiert, et le juste s'en revêt, et l'homme de bien a son argent en partage;
18 Gidan da ya gina kamar gidan gizo-gizo, kamar bukkar mai tsaro.
il bâtit une maison fragile comme celle de la teigne, comme la guérite qu'élève le garde-champêtre;
19 Attajiri zai kwanta, amma daga wannan shi ke nan; lokacin da zai buɗe idanunsa, kome ya tafi.
riche il se couche, et il ne se relève pas; il ouvre les yeux, et il n'est plus.
20 Tsoro zai kwashe shi kamar ambaliyar ruwa; Da dare iska za tă tafi da shi.
Comme des eaux les terreurs l'atteignent, la nuit l'ouragan le dérobe,
21 Iskar gabas za tă tafi da shi; shi ke nan ya ƙare; za tă share shi daga wurinsa.
le vent d'orient l'enlève et part, et dans un tourbillon le porte loin de ses lieux.
22 Za tă murɗe shi ba tausayi, lokacin da yake guje wa ikon iskar.
[Dieu] tire sur lui sans pitié il voudrait par la fuite échapper à Sa main.
23 Zai tafa hannu yă yi tsaki yă kawar da shi daga wurinsa.”
On l'accompagne de battements de mains et de sifflements, quand il quitte ses lieux.