< Ayuba 27 >

1 Ayuba kuwa ya ci gaba da magana,
Et Job reprit son discours sentencieux et dit:
2 “Na rantse da Allah mai rai, wanda ya danne mini gaskiyata, Maɗaukaki, wanda ya sa nake cikin ɗacin rai.
Dieu qui a écarté mon droit, le Tout-puissant qui met l’amertume dans mon âme, est vivant:
3 Muddin ina da rai a cikina kuma numfashin Allah yana cikin hancina,
Tant que mon souffle est en moi et l’esprit de Dieu dans mes narines,
4 bakina ba zai faɗi mugun abu ba, harshena kuma ba zai yi ƙarya ba.
Mes lèvres ne diront pas d’iniquité, et ma langue ne prononcera pas de fausseté.
5 Ba zan taɓa yarda cewa kuna da gaskiya ba; har in mutu, ba zan daina kāre mutuncina ba.
Loin de moi que je vous justifie! Jusqu’à ce que j’expire, je ne lâcherai pas ma perfection;
6 Zan ci gaba da adalcina, ba zan fasa ba; lamirina ba zai taɓa yashe ni ba, dukan kwanakin raina.
Je tiendrai ferme ma justice et je n’en ferai pas abandon; mon cœur ne me reproche aucun de mes jours.
7 “Bari maƙiyana su zama kamar mugaye, masu gāba da ni kuma su zama kamar marasa adalci.
Que mon ennemi soit comme le méchant, et celui qui s’élève contre moi comme l’inique!
8 Gama wane bege marar tsoron Allah yake da shi, lokacin da aka datse shi, lokacin da Allah ya ɗauke ransa?
Car quelle est l’espérance de l’impie quand [Dieu le] retranche, quand Dieu retire son âme?
9 Ko Allah yana sauraron kukansa lokacin da ƙunci ya auko masa?
Dieu entendra-t-il son cri quand la détresse viendra sur lui?
10 Ko zai sami farin ciki daga Maɗaukaki? Ko zai yi kira ga Allah a kowane lokaci?
Trouvera-t-il ses délices dans le Tout-puissant? Invoquera-t-il Dieu en tout temps?
11 “Zan koya muku game da ikon Allah; ba zan ɓoye hanyoyin Maɗaukaki ba.
Je vous enseignerai comment Dieu agit, je ne cacherai pas ce qui est par-devers le Tout-puissant.
12 Duk kun ga wannan ku da kanku saboda haka me ya sa kuke maganganun nan marasa ma’ana?
Voici, vous-mêmes, vous l’avez tous vu: et pourquoi entretenez-vous ces vaines pensées?
13 “Ga abin da mugaye za su samu gādon da azzalumi zai samu daga Maɗaukaki.
Voici quelle est, par-devers Dieu, la part de l’homme méchant et l’héritage que les violents reçoivent du Tout-puissant:
14 Kome yawan’ya’yansa, takobi za tă gama da su; zuriyarsa ba za su taɓa samun isashen abinci ba.
Si ses fils se multiplient, c’est pour l’épée, et ses descendants ne sont pas rassasiés de pain.
15 Waɗanda suka tsira annoba za tă kashe su, kuma gwaurayensu ba za su yi kukan mutuwarsu ba.
Ceux qui restent après lui seront enterrés dans la mort, et ses veuves ne pleureront pas.
16 Ko da yake ya tara azurfa kamar ƙasa, tufafi kuma kamar tarin ƙasa,
S’il entasse l’argent comme la poussière et se prépare des vêtements comme de la boue,
17 abin da ya tara masu adalci za su sa marasa laifi za su raba azurfarsa.
Il se les prépare, mais le juste s’en vêtira; et l’argent, c’est l’innocent qui se le partagera.
18 Gidan da ya gina kamar gidan gizo-gizo, kamar bukkar mai tsaro.
Il a bâti sa maison comme la teigne, comme une cabane que fait celui qui garde [les vignes].
19 Attajiri zai kwanta, amma daga wannan shi ke nan; lokacin da zai buɗe idanunsa, kome ya tafi.
Il se couche riche, et il ne le refera pas; il ouvre ses yeux, et il n’est plus.
20 Tsoro zai kwashe shi kamar ambaliyar ruwa; Da dare iska za tă tafi da shi.
Les frayeurs le surprennent comme des eaux; l’ouragan l’emporte de nuit;
21 Iskar gabas za tă tafi da shi; shi ke nan ya ƙare; za tă share shi daga wurinsa.
Le vent d’orient l’enlève, et il s’en va, et dans un tourbillon il l’emporte de son lieu.
22 Za tă murɗe shi ba tausayi, lokacin da yake guje wa ikon iskar.
[Dieu] lance [ses dards] sur lui et ne l’épargne pas; il voudrait fuir loin de sa main.
23 Zai tafa hannu yă yi tsaki yă kawar da shi daga wurinsa.”
On battra des mains sur lui, et on le chassera de son lieu avec des sifflements.

< Ayuba 27 >