< Ayuba 27 >
1 Ayuba kuwa ya ci gaba da magana,
And Job addeth to lift up his simile, and saith: —
2 “Na rantse da Allah mai rai, wanda ya danne mini gaskiyata, Maɗaukaki, wanda ya sa nake cikin ɗacin rai.
God liveth! He turned aside my judgment, And the Mighty — He made my soul bitter.
3 Muddin ina da rai a cikina kuma numfashin Allah yana cikin hancina,
For all the while my breath [is] in me, And the spirit of God in my nostrils.
4 bakina ba zai faɗi mugun abu ba, harshena kuma ba zai yi ƙarya ba.
My lips do not speak perverseness, And my tongue doth not utter deceit.
5 Ba zan taɓa yarda cewa kuna da gaskiya ba; har in mutu, ba zan daina kāre mutuncina ba.
Pollution to me — if I justify you, Till I expire I turn not aside mine integrity from me.
6 Zan ci gaba da adalcina, ba zan fasa ba; lamirina ba zai taɓa yashe ni ba, dukan kwanakin raina.
On my righteousness I have laid hold, And I do not let it go, My heart doth not reproach me while I live.
7 “Bari maƙiyana su zama kamar mugaye, masu gāba da ni kuma su zama kamar marasa adalci.
As the wicked is my enemy, And my withstander as the perverse.
8 Gama wane bege marar tsoron Allah yake da shi, lokacin da aka datse shi, lokacin da Allah ya ɗauke ransa?
For what [is] the hope of the profane, When He doth cut off? When God doth cast off his soul?
9 Ko Allah yana sauraron kukansa lokacin da ƙunci ya auko masa?
His cry doth God hear, When distress cometh on him?
10 Ko zai sami farin ciki daga Maɗaukaki? Ko zai yi kira ga Allah a kowane lokaci?
On the Mighty doth he delight himself? Call God at all times?
11 “Zan koya muku game da ikon Allah; ba zan ɓoye hanyoyin Maɗaukaki ba.
I shew you by the hand of God, That which [is] with the Mighty I hide not.
12 Duk kun ga wannan ku da kanku saboda haka me ya sa kuke maganganun nan marasa ma’ana?
Lo, ye — all of you — have seen, And why [is] this — ye are altogether vain?
13 “Ga abin da mugaye za su samu gādon da azzalumi zai samu daga Maɗaukaki.
This [is] the portion of wicked man with God, And the inheritance of terrible ones From the Mighty they receive.
14 Kome yawan’ya’yansa, takobi za tă gama da su; zuriyarsa ba za su taɓa samun isashen abinci ba.
If his sons multiply — for them [is] a sword. And his offspring [are] not satisfied [with] bread.
15 Waɗanda suka tsira annoba za tă kashe su, kuma gwaurayensu ba za su yi kukan mutuwarsu ba.
His remnant in death are buried, And his widows do not weep.
16 Ko da yake ya tara azurfa kamar ƙasa, tufafi kuma kamar tarin ƙasa,
If he heap up as dust silver, And as clay prepare clothing,
17 abin da ya tara masu adalci za su sa marasa laifi za su raba azurfarsa.
He prepareth — and the righteous putteth [it] on, And the silver the innocent doth apportion.
18 Gidan da ya gina kamar gidan gizo-gizo, kamar bukkar mai tsaro.
He hath built as a moth his house, And as a booth a watchman hath made.
19 Attajiri zai kwanta, amma daga wannan shi ke nan; lokacin da zai buɗe idanunsa, kome ya tafi.
Rich he lieth down, and he is not gathered, His eyes he hath opened, and he is not.
20 Tsoro zai kwashe shi kamar ambaliyar ruwa; Da dare iska za tă tafi da shi.
Overtake him as waters do terrors, By night stolen him away hath a whirlwind.
21 Iskar gabas za tă tafi da shi; shi ke nan ya ƙare; za tă share shi daga wurinsa.
Take him up doth an east wind, and he goeth, And it frighteneth him from his place,
22 Za tă murɗe shi ba tausayi, lokacin da yake guje wa ikon iskar.
And it casteth at him, and doth not spare, From its hand he diligently fleeth.
23 Zai tafa hannu yă yi tsaki yă kawar da shi daga wurinsa.”
It clappeth at him its hands, And it hisseth at him from his place.