< Ayuba 27 >

1 Ayuba kuwa ya ci gaba da magana,
And Job again took up his measure, and said: —
2 “Na rantse da Allah mai rai, wanda ya danne mini gaskiyata, Maɗaukaki, wanda ya sa nake cikin ɗacin rai.
As GOD liveth who hath taken away my right, even the Almighty, who hath embittered my soul;
3 Muddin ina da rai a cikina kuma numfashin Allah yana cikin hancina,
All the while my inspiration is in me, and the spirit of GOD is in my nostrils,
4 bakina ba zai faɗi mugun abu ba, harshena kuma ba zai yi ƙarya ba.
Verily my lips shall not speak perversity, nor shall, my tongue, utter deceit.
5 Ba zan taɓa yarda cewa kuna da gaskiya ba; har in mutu, ba zan daina kāre mutuncina ba.
Far be it from me! that I should justify, you, —Even until I breathe my last, will I not let go mine integrity from me:
6 Zan ci gaba da adalcina, ba zan fasa ba; lamirina ba zai taɓa yashe ni ba, dukan kwanakin raina.
On my righteousness, have I taken fast hold, and will not give it up, My heart shall not reproach any of my days.
7 “Bari maƙiyana su zama kamar mugaye, masu gāba da ni kuma su zama kamar marasa adalci.
Let mine enemy be a veritably lawless one! And, he that lifteth himself up against me, one veritably perverse!
8 Gama wane bege marar tsoron Allah yake da shi, lokacin da aka datse shi, lokacin da Allah ya ɗauke ransa?
For what shall be the hope of the impious, though he graspeth with greed, when GOD shall draw forth his soul?
9 Ko Allah yana sauraron kukansa lokacin da ƙunci ya auko masa?
His outcry, will GOD hear, when there cometh upon him distress?
10 Ko zai sami farin ciki daga Maɗaukaki? Ko zai yi kira ga Allah a kowane lokaci?
Verily, in the Almighty, he will not find delight, nor call on GOD continually!
11 “Zan koya muku game da ikon Allah; ba zan ɓoye hanyoyin Maɗaukaki ba.
I would teach you, by the hand of GOD, That which is with the Almighty, will I not conceal.
12 Duk kun ga wannan ku da kanku saboda haka me ya sa kuke maganganun nan marasa ma’ana?
Lo! ye, have, all of you, seen, Wherefore, then, is it, that ye are utterly without purpose?
13 “Ga abin da mugaye za su samu gādon da azzalumi zai samu daga Maɗaukaki.
This, is the portion of a lawless man with GOD, That, the heritage of tyrants—from the Almighty, he shall receive.
14 Kome yawan’ya’yansa, takobi za tă gama da su; zuriyarsa ba za su taɓa samun isashen abinci ba.
If his children be multiplied, for them, [there is] the sword, and, his offspring, shall not be filled with bread;
15 Waɗanda suka tsira annoba za tă kashe su, kuma gwaurayensu ba za su yi kukan mutuwarsu ba.
His survivors, by pestilence, shall come to the grave, and, his widows, shall not weep;
16 Ko da yake ya tara azurfa kamar ƙasa, tufafi kuma kamar tarin ƙasa,
Though he heap up silver like, dust, and, like a pile, he prepare clothing,
17 abin da ya tara masu adalci za su sa marasa laifi za su raba azurfarsa.
He may prepare, but, the righteous, shall put on, and, the silver, shall the innocent apportion.
18 Gidan da ya gina kamar gidan gizo-gizo, kamar bukkar mai tsaro.
He hath built, like a moth, his house, —like a hut, which a watcher hath made.
19 Attajiri zai kwanta, amma daga wannan shi ke nan; lokacin da zai buɗe idanunsa, kome ya tafi.
The rich man, shall lie down, and not do it again, his eyes, hath he opened, and then is not.
20 Tsoro zai kwashe shi kamar ambaliyar ruwa; Da dare iska za tă tafi da shi.
There shall reach him—like waters—terrors, By night, a storm-wind hath stolen him away;
21 Iskar gabas za tă tafi da shi; shi ke nan ya ƙare; za tă share shi daga wurinsa.
An east wind shall lift him up, and he shall depart, and it shall sweep him away out of his place;
22 Za tă murɗe shi ba tausayi, lokacin da yake guje wa ikon iskar.
And He will cast upon him and not spare, Out of his hand, shall he, swiftly flee;
23 Zai tafa hannu yă yi tsaki yă kawar da shi daga wurinsa.”
He shall clap over him his hands, and shall hiss him forth out of his place.

< Ayuba 27 >