< Ayuba 27 >

1 Ayuba kuwa ya ci gaba da magana,
Job vedblev at fremsætte sit Tankesprog:
2 “Na rantse da Allah mai rai, wanda ya danne mini gaskiyata, Maɗaukaki, wanda ya sa nake cikin ɗacin rai.
"Så sandt Gud lever, som satte min Ret til Side, den Almægtige, som gjorde mig mod i Hu:
3 Muddin ina da rai a cikina kuma numfashin Allah yana cikin hancina,
Så længe jeg drager Ånde og har Guds Ånde i Næsen,
4 bakina ba zai faɗi mugun abu ba, harshena kuma ba zai yi ƙarya ba.
skal mine Læber ej tale Uret, min Tunge ej fare med Svig!
5 Ba zan taɓa yarda cewa kuna da gaskiya ba; har in mutu, ba zan daina kāre mutuncina ba.
Langt være det fra mig at give jer Ret; til jeg udånder, opgiver jeg ikke min Uskyld.
6 Zan ci gaba da adalcina, ba zan fasa ba; lamirina ba zai taɓa yashe ni ba, dukan kwanakin raina.
Jeg hævder min Ret, jeg slipper den ikke, ingen af mine Dage piner mit Sind.
7 “Bari maƙiyana su zama kamar mugaye, masu gāba da ni kuma su zama kamar marasa adalci.
Som den gudløse gå det min Fjende, min Modstander som den lovløse!
8 Gama wane bege marar tsoron Allah yake da shi, lokacin da aka datse shi, lokacin da Allah ya ɗauke ransa?
Thi hvad er den vanhelliges Håb, når Gud bortskærer og kræver hans Sjæl?
9 Ko Allah yana sauraron kukansa lokacin da ƙunci ya auko masa?
Hører mon Gud hans Skrig, når Angst kommer over ham?
10 Ko zai sami farin ciki daga Maɗaukaki? Ko zai yi kira ga Allah a kowane lokaci?
Mon han kan fryde sig over den Almægtige, føjer han ham, når han påkalder ham?
11 “Zan koya muku game da ikon Allah; ba zan ɓoye hanyoyin Maɗaukaki ba.
Jeg vil lære jer om Guds Hånd, den Almægtiges Tanker dølger jeg ikke;
12 Duk kun ga wannan ku da kanku saboda haka me ya sa kuke maganganun nan marasa ma’ana?
se, selv har I alle set det, hvi har I så tomme Tanker?
13 “Ga abin da mugaye za su samu gādon da azzalumi zai samu daga Maɗaukaki.
Det er den gudløses Lod fra Gud, Arven, som Voldsmænd får fra den Almægtige:
14 Kome yawan’ya’yansa, takobi za tă gama da su; zuriyarsa ba za su taɓa samun isashen abinci ba.
Vokser hans Sønner, er det for Sværdet, hans Afkom mættes ikke med Brød;
15 Waɗanda suka tsira annoba za tă kashe su, kuma gwaurayensu ba za su yi kukan mutuwarsu ba.
de øvrige bringer Pesten i Graven, deres Enker kan ej holde Klage over dem.
16 Ko da yake ya tara azurfa kamar ƙasa, tufafi kuma kamar tarin ƙasa,
Opdynger han Sølv som Støv og samler sig Klæder som Ler
17 abin da ya tara masu adalci za su sa marasa laifi za su raba azurfarsa.
han samler, men den retfærdige klæder sig i dem, og Sølvet arver den skyldfri;
18 Gidan da ya gina kamar gidan gizo-gizo, kamar bukkar mai tsaro.
han bygger sit Hus som en Edderkops, som Hytten, en Vogter gør sig;
19 Attajiri zai kwanta, amma daga wannan shi ke nan; lokacin da zai buɗe idanunsa, kome ya tafi.
han lægger sig rig, men for sidste ang, han slår Øjnene op, og er det ej mer;
20 Tsoro zai kwashe shi kamar ambaliyar ruwa; Da dare iska za tă tafi da shi.
Rædsler når ham som Vande, ved Nat river Stormen ham bort;
21 Iskar gabas za tă tafi da shi; shi ke nan ya ƙare; za tă share shi daga wurinsa.
løftet af Østenstorm farer han bort, den fejer ham væk fra hans Sted.
22 Za tă murɗe shi ba tausayi, lokacin da yake guje wa ikon iskar.
Skånselsløst skyder han på ham, i Hast må han fly fra hans Hånd;
23 Zai tafa hannu yă yi tsaki yă kawar da shi daga wurinsa.”
man klapper i Hænderne mod ham og piber ham bort fra hans Sted!

< Ayuba 27 >