< Ayuba 26 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Felelt Jób és mondta:
2 “Yadda ka taimaki marar ƙarfi! Yadda ka ceci marar ƙarfi!
Mint gyámolítottad a tehetetlent, segítetted az erőtlennek karját!
3 Ka ba marar hikima shawara! Ka nuna kana da ilimi sosai.
Mit tanácsoltál a bölcsességtelennek s valódi tudást bőven ismertettél!
4 Wane ne ya taimake ka ka yi waɗannan maganganu? Kuma ruhun wane ne ya yi magana ta bakinka?
Kinek adtál tudtul szavakat s kinek szelleme fakadt belőled?
5 “Matattu suna cikin azaba, waɗanda suke ƙarƙashin ruwaye da dukan mazauna cikin ruwaye.
Az árnyak megreszketnek alul a vizeken és lakóikon.
6 Mutuwa tsirara take a gaban Allah; haka kuma hallaka take a buɗe. (Sheol h7585)
Meztelen az alvilág ő előtte s takarója az enyészet neki. (Sheol h7585)
7 Ya shimfiɗa arewancin sararin sama a sarari; ya rataye duniya ba a jikin wani abu ba.
Kiterjeszti az Északot az űr fölé, lebegteti a földet a semmiségen;
8 Ya naɗe ruwaye a cikin gizagizansa, duk da haka girgijen bai yage saboda nauyi ba.
beköti a vizet felhőibe, s nem hasad meg felleg alatta;
9 Ya rufe fuskar wata, ya shimfiɗa gizagizai a kan shi,
befogja a trón felszínét, kiterítette reá fellegét.
10 ya zāna iyakar fuskar ruwa a kan iyakar da take tsakanin duhu da haske.
Határt vont a vizek színén odáig, hol vége van a világosságnak a sötétség mellett.
11 Madogaran sama sun girgiza, saboda tsawatawarsa.
Az ég oszlopai megrázkódnak s elámulnak dorgálásától.
12 Da ikonsa ya kwantar da teku; da hikimarsa ya hallaka dodon ruwan nan Rahab.
Erejével felkavarta a tengert s értelmével összezúzta, Ráhábot.
13 Da numfashinsa ya sa sararin sama ya yi kyau da hannunsa ya soke macijin nan mai gudu.
Fuvallata által derültté válik az ég, átszúrta keze a futó kígyót.
14 Waɗannan kaɗan ke nan daga cikin ayyukansa masu yawa. Kaɗan kawai muke ji game da shi! Wane ne kuwa yake iya gane tsawar ikonsa?”
Lám, ezek útjainak szélei, mily csekély nesz az, a mit róla hallunk, de hatalmának dörgését ki foghatja föl!

< Ayuba 26 >