< Ayuba 26 >
Und Hiob antwortete und sprach:
2 “Yadda ka taimaki marar ƙarfi! Yadda ka ceci marar ƙarfi!
Wie hast du doch den Ohnmächtigen unterstützt und dem machtlosen Arm geholfen!
3 Ka ba marar hikima shawara! Ka nuna kana da ilimi sosai.
Wie hast du den Unweisen beraten und Weisheit in Fülle kundgetan!
4 Wane ne ya taimake ka ka yi waɗannan maganganu? Kuma ruhun wane ne ya yi magana ta bakinka?
Wen hast du mit deiner Rede getroffen und wessen Odem ging aus deinem Munde hervor?
5 “Matattu suna cikin azaba, waɗanda suke ƙarƙashin ruwaye da dukan mazauna cikin ruwaye.
Die Schatten werden von Zittern erfaßt unter den Wassern und ihren Bewohnern.
6 Mutuwa tsirara take a gaban Allah; haka kuma hallaka take a buɗe. (Sheol )
Das Totenreich ist enthüllt vor Ihm, und der Abgrund hat keine Decke. (Sheol )
7 Ya shimfiɗa arewancin sararin sama a sarari; ya rataye duniya ba a jikin wani abu ba.
Er spannt den Norden aus über der Leere und hängt die Erde über dem Nichts auf.
8 Ya naɗe ruwaye a cikin gizagizansa, duk da haka girgijen bai yage saboda nauyi ba.
Er bindet die Wasser in seinen Wolken zusammen, und das Gewölk zerbricht nicht unter ihrem Gewicht.
9 Ya rufe fuskar wata, ya shimfiɗa gizagizai a kan shi,
Er verschließt den Anblick seines Thrones, er breitet seine Wolken darüber.
10 ya zāna iyakar fuskar ruwa a kan iyakar da take tsakanin duhu da haske.
Er hat einen Kreis abgesteckt auf der Oberfläche der Wasser, zur Grenze des Lichts und der Finsternis.
11 Madogaran sama sun girgiza, saboda tsawatawarsa.
Des Himmels Säulen erbeben und zittern vor seinem Schelten.
12 Da ikonsa ya kwantar da teku; da hikimarsa ya hallaka dodon ruwan nan Rahab.
Durch seine Kraft erregt er das Meer, und mit seinem Verstand zerschlägt er das Ungeheuer.
13 Da numfashinsa ya sa sararin sama ya yi kyau da hannunsa ya soke macijin nan mai gudu.
Durch seinen Hauch wird der Himmel klar, mit seiner Hand durchbohrt er die flüchtige Schlange.
14 Waɗannan kaɗan ke nan daga cikin ayyukansa masu yawa. Kaɗan kawai muke ji game da shi! Wane ne kuwa yake iya gane tsawar ikonsa?”
Siehe, das sind die Umrisse seiner Wege; wie leise ist das Wort, das wir davon vernehmen! Wer will aber den Donner seiner Macht verstehen?