< Ayuba 26 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Da antwortete Hiob folgendermaßen:
2 “Yadda ka taimaki marar ƙarfi! Yadda ka ceci marar ƙarfi!
»Wie hast du doch dem Schwachen beigestanden und den kraftlosen Arm gestützt!
3 Ka ba marar hikima shawara! Ka nuna kana da ilimi sosai.
Wie gut hast du doch den Unweisen beraten und tiefes Wissen in Fülle kundgetan!
4 Wane ne ya taimake ka ka yi waɗannan maganganu? Kuma ruhun wane ne ya yi magana ta bakinka?
Wem hast du einen Lehrvortrag gehalten, und wessen Odem ist dir entströmt?«
5 “Matattu suna cikin azaba, waɗanda suke ƙarƙashin ruwaye da dukan mazauna cikin ruwaye.
»Die Schatten erzittern (vor Gott) tief unter den Wassern und deren Bewohnern;
6 Mutuwa tsirara take a gaban Allah; haka kuma hallaka take a buɗe. (Sheol h7585)
nackt liegt das Totenreich vor ihm da und unverhüllt der Abgrund. (Sheol h7585)
7 Ya shimfiɗa arewancin sararin sama a sarari; ya rataye duniya ba a jikin wani abu ba.
Er spannt den Norden (der Erde) über der Leere aus, hängt die Erde an dem Nichts auf.
8 Ya naɗe ruwaye a cikin gizagizansa, duk da haka girgijen bai yage saboda nauyi ba.
Er bindet die Wasser in seine Wolken ein, ohne daß das Gewölk unter ihrer Last zerplatzt.
9 Ya rufe fuskar wata, ya shimfiɗa gizagizai a kan shi,
Er verhüllt den Anblick seines Thrones, indem er sein Gewölk über ihn ausbreitet.
10 ya zāna iyakar fuskar ruwa a kan iyakar da take tsakanin duhu da haske.
Eine Grenzlinie hat er über den weiten Wassern abgezirkelt bis zur äußersten Grenze, wo das Licht mit der Finsternis zusammentrifft.
11 Madogaran sama sun girgiza, saboda tsawatawarsa.
Die Säulen des Himmels geraten ins Wanken und beben infolge seines Scheltens.
12 Da ikonsa ya kwantar da teku; da hikimarsa ya hallaka dodon ruwan nan Rahab.
Durch seine Kraft beruhigt er das Meer, und durch seine Klugheit hat er Rahab zerschmettert.
13 Da numfashinsa ya sa sararin sama ya yi kyau da hannunsa ya soke macijin nan mai gudu.
Durch seinen Hauch gewinnt der Himmel Heiterkeit; durchbohrt hat seine Hand den flüchtigen Drachen.
14 Waɗannan kaɗan ke nan daga cikin ayyukansa masu yawa. Kaɗan kawai muke ji game da shi! Wane ne kuwa yake iya gane tsawar ikonsa?”
Siehe, das sind nur die Säume seines Waltens, und welch ein leises Flüstern nur ist es, das wir von ihm vernehmen! Doch die Donnersprache seiner Machterweise – wer versteht diese?«

< Ayuba 26 >