< Ayuba 26 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Hiob antwortete und sprach:
2 “Yadda ka taimaki marar ƙarfi! Yadda ka ceci marar ƙarfi!
Wie trefflich hast du der Ohnmacht geholfen, den kraftlosen Arm gestützt,
3 Ka ba marar hikima shawara! Ka nuna kana da ilimi sosai.
wie trefflich den Unverständigen beraten und Weisheit in Fülle geoffenbart!
4 Wane ne ya taimake ka ka yi waɗannan maganganu? Kuma ruhun wane ne ya yi magana ta bakinka?
Wem hast du deine Reden vorgetragen, und wessen Geist hat aus dir gesprochen?
5 “Matattu suna cikin azaba, waɗanda suke ƙarƙashin ruwaye da dukan mazauna cikin ruwaye.
Die Schatten selbst werden in Beben versetzt unter den Wassern und ihren Bewohnern.
6 Mutuwa tsirara take a gaban Allah; haka kuma hallaka take a buɗe. (Sheol h7585)
Nackt liegt die Unterwelt vor ihm, und unverhüllt der Abgrund. (Sheol h7585)
7 Ya shimfiɗa arewancin sararin sama a sarari; ya rataye duniya ba a jikin wani abu ba.
Er spannt den Norden über dem Leeren aus, läßt die Erde schweben über dem Nichts.
8 Ya naɗe ruwaye a cikin gizagizansa, duk da haka girgijen bai yage saboda nauyi ba.
Er bindet die Wasser in seine Wolken ein, ohne daß unter ihnen das Gewölk zerreißt.
9 Ya rufe fuskar wata, ya shimfiɗa gizagizai a kan shi,
Er verhüllt den Anblick seines Throns, indem er sein Gewölk darüber breitet.
10 ya zāna iyakar fuskar ruwa a kan iyakar da take tsakanin duhu da haske.
Eine Grenze zog er über den Wassern hin, da, wo sich scheiden Licht und Finsternis.
11 Madogaran sama sun girgiza, saboda tsawatawarsa.
Des Himmels Säulen werden ins Wanken gebracht und entsetzen sich vor seinem Dräun.
12 Da ikonsa ya kwantar da teku; da hikimarsa ya hallaka dodon ruwan nan Rahab.
Durch seine Macht hat er das Meer erregt und durch seine Einsicht Rahab zerschmettert.
13 Da numfashinsa ya sa sararin sama ya yi kyau da hannunsa ya soke macijin nan mai gudu.
Durch seinen Hauch wird der Himmel heiter, seine Hand durchbohrte den flüchtigen Drachen.
14 Waɗannan kaɗan ke nan daga cikin ayyukansa masu yawa. Kaɗan kawai muke ji game da shi! Wane ne kuwa yake iya gane tsawar ikonsa?”
Und das sind nur die Säume seines Waltens - welch' leis Geflüster nur, das wir vernehmen! Doch wer erfaßt die Donnersprache seiner Allgewalt!

< Ayuba 26 >