< Ayuba 26 >
Darauf erwidert Job und spricht:
2 “Yadda ka taimaki marar ƙarfi! Yadda ka ceci marar ƙarfi!
"Wie trefflich hilfst du doch dem Schwachen und stärkst den Arm den Kraftlosen!
3 Ka ba marar hikima shawara! Ka nuna kana da ilimi sosai.
Welch feinen Rat gibst du der Unweisheit und offenbarst dem Zweifler soviel Kluges!
4 Wane ne ya taimake ka ka yi waɗannan maganganu? Kuma ruhun wane ne ya yi magana ta bakinka?
Wen hast du denn belehren wollen? Und wessen Geist geht von dir aus?
5 “Matattu suna cikin azaba, waɗanda suke ƙarƙashin ruwaye da dukan mazauna cikin ruwaye.
Die Schatten in der Unterwelt geraten außer sich, die Wasser und die sie bewohnen. -
6 Mutuwa tsirara take a gaban Allah; haka kuma hallaka take a buɗe. (Sheol )
Die Unterwelt liegt nackt vor ihm und hüllenlos das Totenreich. (Sheol )
7 Ya shimfiɗa arewancin sararin sama a sarari; ya rataye duniya ba a jikin wani abu ba.
Er spannt den Bären aus im Leeren und läßt die Erde schweben überm Nichts.
8 Ya naɗe ruwaye a cikin gizagizansa, duk da haka girgijen bai yage saboda nauyi ba.
Gewässer bindet er in seine Wolken; nicht reißt darunter das Gewölk.
9 Ya rufe fuskar wata, ya shimfiɗa gizagizai a kan shi,
Er überzieht des Vollmonds Scheibe, darüber breitend sein Gewölk.
10 ya zāna iyakar fuskar ruwa a kan iyakar da take tsakanin duhu da haske.
Und eine Grenze zieht er über den Gewässern, dort wo sich treffen Licht und Finsternis.
11 Madogaran sama sun girgiza, saboda tsawatawarsa.
Des Himmels feste Säulen schwanken; vor seinem Drohen wanken sie.
12 Da ikonsa ya kwantar da teku; da hikimarsa ya hallaka dodon ruwan nan Rahab.
Durch seine Kraft weckt er den Ozean; sein Ungestüm bricht er durch seine Klugheit.
13 Da numfashinsa ya sa sararin sama ya yi kyau da hannunsa ya soke macijin nan mai gudu.
Durch seinen Geist besteht des Himmels Schöne, und seine Hand erschuf die flücht'ge Schlange.
14 Waɗannan kaɗan ke nan daga cikin ayyukansa masu yawa. Kaɗan kawai muke ji game da shi! Wane ne kuwa yake iya gane tsawar ikonsa?”
Das sind nur seines Waltens Säume und nur ein Weniges, was wir so von ihm hören. Wer kann da erst die Donnersprache seiner Allgewalt verstehen?"