< Ayuba 26 >
And Job answereth and saith: —
2 “Yadda ka taimaki marar ƙarfi! Yadda ka ceci marar ƙarfi!
What — thou hast helped the powerless, Saved an arm not strong!
3 Ka ba marar hikima shawara! Ka nuna kana da ilimi sosai.
What — thou hast given counsel to the unwise, And wise plans in abundance made known.
4 Wane ne ya taimake ka ka yi waɗannan maganganu? Kuma ruhun wane ne ya yi magana ta bakinka?
With whom hast thou declared words? And whose breath came forth from thee?
5 “Matattu suna cikin azaba, waɗanda suke ƙarƙashin ruwaye da dukan mazauna cikin ruwaye.
The Rephaim are formed, Beneath the waters, also their inhabitants.
6 Mutuwa tsirara take a gaban Allah; haka kuma hallaka take a buɗe. (Sheol )
Naked [is] Sheol over-against Him, And there is no covering to destruction. (Sheol )
7 Ya shimfiɗa arewancin sararin sama a sarari; ya rataye duniya ba a jikin wani abu ba.
Stretching out the north over desolation, Hanging the earth upon nothing,
8 Ya naɗe ruwaye a cikin gizagizansa, duk da haka girgijen bai yage saboda nauyi ba.
Binding up the waters in His thick clouds, And the cloud is not rent under them.
9 Ya rufe fuskar wata, ya shimfiɗa gizagizai a kan shi,
Taking hold of the face of the throne, Spreading over it His cloud.
10 ya zāna iyakar fuskar ruwa a kan iyakar da take tsakanin duhu da haske.
A limit He hath placed on the waters, Unto the boundary of light with darkness.
11 Madogaran sama sun girgiza, saboda tsawatawarsa.
Pillars of the heavens do tremble, And they wonder because of His rebuke.
12 Da ikonsa ya kwantar da teku; da hikimarsa ya hallaka dodon ruwan nan Rahab.
By His power He hath quieted the sea, And by His understanding smitten the proud.
13 Da numfashinsa ya sa sararin sama ya yi kyau da hannunsa ya soke macijin nan mai gudu.
By His Spirit the heavens He beautified, Formed hath His hand the fleeing serpent.
14 Waɗannan kaɗan ke nan daga cikin ayyukansa masu yawa. Kaɗan kawai muke ji game da shi! Wane ne kuwa yake iya gane tsawar ikonsa?”
Lo, these [are] the borders of His way, And how little a matter is heard of Him, And the thunder of His might Who doth understand?