< Ayuba 26 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Da svarede Job og sagde:
2 “Yadda ka taimaki marar ƙarfi! Yadda ka ceci marar ƙarfi!
Hvad har du hjulpet den, som ingen Kraft havde? frelste du den Arm, som ingen Styrke havde?
3 Ka ba marar hikima shawara! Ka nuna kana da ilimi sosai.
Hvorledes raadede du den, som ingen Visdom havde, og kundgjorde Indsigt til Overflod?
4 Wane ne ya taimake ka ka yi waɗannan maganganu? Kuma ruhun wane ne ya yi magana ta bakinka?
For hvem har du kundgjort Tale, og hvis Aande talte ud af dig?
5 “Matattu suna cikin azaba, waɗanda suke ƙarƙashin ruwaye da dukan mazauna cikin ruwaye.
Dødningerne bæve neden under Vandene og deres Beboere.
6 Mutuwa tsirara take a gaban Allah; haka kuma hallaka take a buɗe. (Sheol h7585)
Dødsriget ligger blottet for ham, og Afgrunden har intet Skjul. (Sheol h7585)
7 Ya shimfiɗa arewancin sararin sama a sarari; ya rataye duniya ba a jikin wani abu ba.
Han udbreder Norden over det øde, han hænger Jorden paa intet.
8 Ya naɗe ruwaye a cikin gizagizansa, duk da haka girgijen bai yage saboda nauyi ba.
Han binder Vandet sammen i sine Skyer, dog brister Skydækket ikke under dem.
9 Ya rufe fuskar wata, ya shimfiɗa gizagizai a kan shi,
Han lukker for sin Trone, han udbreder sin Sky over den.
10 ya zāna iyakar fuskar ruwa a kan iyakar da take tsakanin duhu da haske.
Han har draget en Grænse oven over Vandene indtil der, hvor Lyset ender i Mørke.
11 Madogaran sama sun girgiza, saboda tsawatawarsa.
Himmelens Piller skælve og forfærdes for hans Trusel.
12 Da ikonsa ya kwantar da teku; da hikimarsa ya hallaka dodon ruwan nan Rahab.
Ved sin Kraft oprører han Havet, og med sin Forstand bryder han dets Hovmod.
13 Da numfashinsa ya sa sararin sama ya yi kyau da hannunsa ya soke macijin nan mai gudu.
Ved hans Aande blive Himlene dejlige; hans Haand gennemborer den flygtende Slange.
14 Waɗannan kaɗan ke nan daga cikin ayyukansa masu yawa. Kaɗan kawai muke ji game da shi! Wane ne kuwa yake iya gane tsawar ikonsa?”
Se, disse ere de yderste Grænser af hans Veje, og hvor svag er Lyden af det Ord, som vi have hørt deraf? Men hans Vældes Torden — hvo forstaar den!

< Ayuba 26 >