< Ayuba 25 >

1 Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
Entonces Bildad el Suhita habló y dijo:
2 “Mulki na Allah ne, dole a ji tsoronsa; yana tafiyar da kome yadda ya kamata a cikin sama.
“El dominio y el temor pertenecen a Dios. Él trae la paz a sus cielos.
3 Za a iya ƙirga rundunarsa? A kan wane ne ba ya haska haskensa?
¿Quién puede contar sus ejércitos? ¿Hay algún lugar donde no brille su luz?
4 Ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah? Ta yaya mutumin da mace ta haifa zai zama mai tsarki?
¿Cómo puede un ser humano ser justo ante Dios? ¿Puede alguien nacido de mujer ser puro?
5 In har wata da taurari ba su da tsarki a idanunsa,
Si a los ojos de Dios ni siquiera la luna brilla, y las estrellas no son puras,
6 mutum fa? Ai, wannan tsutsa ne, ɗan ƙwaro kawai. Me mutum ya daɗa a gaban Allah!”
¡cuánto menos un ser humano, que en comparación es como un gusano o una lombriz!”

< Ayuba 25 >