< Ayuba 25 >

1 Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
Und Bildad, der Schuchiter, antwortete und sprach:
2 “Mulki na Allah ne, dole a ji tsoronsa; yana tafiyar da kome yadda ya kamata a cikin sama.
Herrschaft und Schrecken sind bei ihm; er schafft Frieden in seinen Höhen.
3 Za a iya ƙirga rundunarsa? A kan wane ne ba ya haska haskensa?
Sind seine Scharen zu zählen? Und über wem erhebt sich nicht sein Licht?
4 Ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah? Ta yaya mutumin da mace ta haifa zai zama mai tsarki?
Und wie könnte ein Mensch gerecht sein vor Gott, und wie könnte rein sein ein vom Weibe Geborener?
5 In har wata da taurari ba su da tsarki a idanunsa,
Siehe, sogar der Mond scheint nicht hell, und die Sterne sind nicht rein in seinen Augen:
6 mutum fa? Ai, wannan tsutsa ne, ɗan ƙwaro kawai. Me mutum ya daɗa a gaban Allah!”
wieviel weniger der Mensch, der Wurm, und das Menschenkind, die Made!

< Ayuba 25 >