< Ayuba 25 >

1 Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
Then Bildad the Shuhite answered and said,
2 “Mulki na Allah ne, dole a ji tsoronsa; yana tafiyar da kome yadda ya kamata a cikin sama.
“Dominion and fear are with him; he makes order in his high places of heaven.
3 Za a iya ƙirga rundunarsa? A kan wane ne ba ya haska haskensa?
Is there any end to the number of his armies? Upon whom does his light not shine?
4 Ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah? Ta yaya mutumin da mace ta haifa zai zama mai tsarki?
How then can man be righteous with God? How can he who is born of a woman be clean, acceptable to him?
5 In har wata da taurari ba su da tsarki a idanunsa,
See, even the moon has no brightness to him; the stars are not pure in his sight.
6 mutum fa? Ai, wannan tsutsa ne, ɗan ƙwaro kawai. Me mutum ya daɗa a gaban Allah!”
How much less man, who is a worm— a son of man, who is a worm!”

< Ayuba 25 >