< Ayuba 24 >
1 “Domin me Maɗaukaki ba zai sa ranar shari’a ba? Don me waɗanda suka san shi suke faman samun irin ranakun nan?
Czemu, [skoro] od Wszechmocnego nie są zakryte czasy, ci, którzy go znają, nie widzą jego dni?
2 Mugaye suna satar fili ta wurin matsar da duwatsun da aka yi iyaka da su; suna satar dabbobi su kuma yi kiwon su.
[Niektórzy] przesuwają granice, zabierają trzody i pasą je.
3 Suna ƙwace wa marayu jakunansu suna kuma ƙwace wa gwauruwa sa don suna binta bashi.
Osła sierot pędzą i wołu wdowy biorą w zastaw.
4 Suna ture matalauta daga hanya suna kuma sa dole matalautan ƙasar su ɓoye.
Spychają z drogi ubogich, biedni ziemi [muszą] się kryć razem.
5 Kamar jakunan jeji a hamada, matalauta suna aikin neman abinci gonaki marasa amfani suna tanada abinci wa’ya’yansu.
Oto jak dzikie osły na pustyni wychodzą oni do swojej pracy, wstając rano na łup. Pustynia [wydaje] chleb dla nich oraz ich dzieci.
6 Suna girbi a gonakin da ba nasu ba, suna yin kala a gonar inabi ta mugaye.
Na polu żną zboże i zbierają [grona] w winnicy niegodziwych.
7 Don ba su da tufafi, sukan kwana tsirara; ba su da wani abin da zai rufe su cikin sanyi.
Nagich zmuszają nocować bez ubrania, tak że nie mają czym się nakryć w czasie chłodów;
8 Sun jiƙe sharkaf da ruwan da yake kwararowa daga duwatsu, sun rungume duwatsu don rashin wurin fakewa.
Przemoczeni ulewą górską, bez schronienia przytulają się do skały.
9 Ana ƙwace jinjiri mai shan mama; ana ƙwace ɗan yaron matalauci don biyan bashi.
Odrywają od piersi sieroty, od ubogiego biorą zastaw.
10 Don ba su da tufafi suna yawo tsirara; suna dakon dammunan hatsi amma duk da haka suna cikin shan yunwa.
Nagiego zmuszają do chodzenia bez ubrania, a głodnym zabierają snopy.
11 Suna matse zaitun a cikin kunyoyi suna kuma matse ruwan inabi daga’ya’yan inabi, duk da haka suna fama da ƙishi.
[A ci, którzy] pośród ich murów wyciskają oliwę i tłoczą w prasach, są spragnieni.
12 Ana jin nishin masu mutuwa daga birni, kuma rayukan waɗanda aka ji musu rauni suna kuka suna kira don taimako. Amma bai ba wani laifi ba.
Ludzie w mieście wzdychają, dusze śmiertelnie rannych wołają, a Bóg im w tym nie przeszkadza.
13 “Akwai waɗanda suke yi wa haske tawaye, waɗanda ba su san hanyoyinsa ba ko kuma ba su taɓa bin hanyoyinsa ba.
To są ci, którzy się sprzeciwiają światłości, nie znają jej dróg ani nie trwają na jej ścieżkach.
14 Sa’ad da hasken yini ya tafi, mai kisankai yakan tashi; yă je yă kashe matalauta da masu bukata; a cikin dare yake shigowa kamar ɓarawo.
Morderca wstaje przed świtem i zabija ubogiego i potrzebującego, a w nocy jest jak złodziej.
15 Idanun mazinaci suna jiran yamma ta yi sosai; yana tunani cewa, ‘Ba wanda zai gan ni,’ sai kuma yă ɓoye fuskarsa.
Oko cudzołożnika czeka na zmierzch, mówiąc: Nikt mnie nie zobaczy, i zakrywa on [swoje] oblicze.
16 Cikin duhu mutane suna fasa gidaje, amma da rana sukan kulle kansu; ba sa so wani abu yă haɗa su da haske.
W ciemności podkopują domy, które sobie za dnia oznaczyli, nie znają światła.
17 Gama dukansu, duhu mai yawa shi ne safiyarsu; suna abokantaka da razanar duhu.
Dla nich bowiem poranek jest jak cień śmierci. Jeśli ktoś ich rozpozna, ogarnia ich strach cienia śmierci.
18 “Duk da haka kamar abu marar nauyi suke a kan ruwa; gefen ƙasar da suke, an la’anta ta, yadda ba wanda yake zuwa gonar inabinsu.
Lekko unoszą się na wodach, przeklęty jest ich dział na ziemi, nie patrzą na drogę [do] winnic.
19 Kamar yadda zafi da fări suke shanye ƙanƙarar da ta narke, haka kabari zai ƙwace waɗanda suka yi zunubi. (Sheol )
[Jak] susza i upał trawią wody śniegu, [tak] grób [trawi] grzeszników. (Sheol )
20 Waɗanda suka haife su za su manta da su, tsutsotsi za su cinye su; ba za a sāke tunawa da mugaye ba amma an sare su kamar itace.
Zapomni o nim łono [jego] matki, a robak będzie się nim karmić jak słodycz; nikt go więcej nie wspomni, a nieprawość zostanie połamana jak drzewo.
21 Suna cutar macen da ba ta da ɗa, suna nuna wa gwauruwa rashin alheri.
Dręczy niepłodną, która nie rodziła, a wdowie nie czyni dobra.
22 Amma Allah cikin ikonsa yakan kawar da masu ƙarfi, ko da yake sun yi ƙarfi, ba su da tabbacin rayuwa.
Pociąga też mocarzy swoją siłą; [gdy] powstaje, nikt nie jest pewien swego życia.
23 Mai yiwuwa zai bar su su zauna cikin kwanciyar hankali, amma idanunsa suna kansu.
Dano mu, że może oprzeć się bezpiecznie; jego oczy jednak [patrzą] na ich drogi.
24 Sukan samu cin nasara na ɗan lokaci, amma kuma za su ɓace; za su fāɗi a tattara su kamar sauran; za a datse su kamar kan hatsi.
Na chwilę zostali wywyższeni, ale już [ich] nie ma; zostali poniżeni [i] ściśnieni jak wszyscy inni, a jak wierzch kłosa zostaną wycięci.
25 “In wannan ba haka ba ne, wane ne zai shaida ƙarya nake yi har yă ƙi yarda da maganata?”
A jeśli tak nie jest, kto mi udowodni kłamstwo i obróci wniwecz moje słowa?