< Ayuba 24 >
1 “Domin me Maɗaukaki ba zai sa ranar shari’a ba? Don me waɗanda suka san shi suke faman samun irin ranakun nan?
Miért nincsenek eltéve a Mindenható által idők s ismerői nem láthatják meg az ő napjait?
2 Mugaye suna satar fili ta wurin matsar da duwatsun da aka yi iyaka da su; suna satar dabbobi su kuma yi kiwon su.
Határokat tolnak el, nyájat raboltak s legeltették.
3 Suna ƙwace wa marayu jakunansu suna kuma ƙwace wa gwauruwa sa don suna binta bashi.
Árvák szamarát elhajtják, zálogul veszik özvegy marháját.
4 Suna ture matalauta daga hanya suna kuma sa dole matalautan ƙasar su ɓoye.
Az útról elhajtják a szűkölködőket, egyaránt elbújtak az ország szegényei.
5 Kamar jakunan jeji a hamada, matalauta suna aikin neman abinci gonaki marasa amfani suna tanada abinci wa’ya’yansu.
Lám, akár vadszamarak a pusztákban, kimentek dolgukra az eledelt keresve: sivatag neki kenyere a gyermekek számára.
6 Suna girbi a gonakin da ba nasu ba, suna yin kala a gonar inabi ta mugaye.
A mezőn learatják abrakjukat s tallóznak a gonosznak szőlőjében.
7 Don ba su da tufafi, sukan kwana tsirara; ba su da wani abin da zai rufe su cikin sanyi.
Meztelenül hálnak, öltözet híján s nincs takarójuk a hidegben;
8 Sun jiƙe sharkaf da ruwan da yake kwararowa daga duwatsu, sun rungume duwatsu don rashin wurin fakewa.
hegyek záporától átáznak s menedék híján sziklát ölelnek.
9 Ana ƙwace jinjiri mai shan mama; ana ƙwace ɗan yaron matalauci don biyan bashi.
Emlőtől elrabolják az árvát s a mi rajta van a szegényen, zálogul veszik;
10 Don ba su da tufafi suna yawo tsirara; suna dakon dammunan hatsi amma duk da haka suna cikin shan yunwa.
meztelenül járnak öltözet híján s éhesen hordanak kévét.
11 Suna matse zaitun a cikin kunyoyi suna kuma matse ruwan inabi daga’ya’yan inabi, duk da haka suna fama da ƙishi.
Falaik között olajat készítenek, a présházakban sajtoltak és szomjaztak.
12 Ana jin nishin masu mutuwa daga birni, kuma rayukan waɗanda aka ji musu rauni suna kuka suna kira don taimako. Amma bai ba wani laifi ba.
A városból emberek hörögnek, a megöltek lelke könyörög és Isten ügyet sem vet a fonákságára.
13 “Akwai waɗanda suke yi wa haske tawaye, waɗanda ba su san hanyoyinsa ba ko kuma ba su taɓa bin hanyoyinsa ba.
Azok vannak a világosság ellen lázadók közt, nem ismerték fel útjait s nem laktak ösvényein.
14 Sa’ad da hasken yini ya tafi, mai kisankai yakan tashi; yă je yă kashe matalauta da masu bukata; a cikin dare yake shigowa kamar ɓarawo.
Virradatra fölkel a gyilkos, megöli a szegényt és szűkölködőt, éjjel pedig olyan lesz mint a tolvaj.
15 Idanun mazinaci suna jiran yamma ta yi sosai; yana tunani cewa, ‘Ba wanda zai gan ni,’ sai kuma yă ɓoye fuskarsa.
A házasságtörő szeme leste az alkonyatot, mondván nem pillant meg engem szem, és leplet tesz arczára.
16 Cikin duhu mutane suna fasa gidaje, amma da rana sukan kulle kansu; ba sa so wani abu yă haɗa su da haske.
Sötétben betörnek házakba, nappal elzárták magukat, nem ismerik a világosságot;
17 Gama dukansu, duhu mai yawa shi ne safiyarsu; suna abokantaka da razanar duhu.
mert egyaránt reggel nekik a vakhomály, mert ismerik a vakhomály rémségeit.
18 “Duk da haka kamar abu marar nauyi suke a kan ruwa; gefen ƙasar da suke, an la’anta ta, yadda ba wanda yake zuwa gonar inabinsu.
Gyorsan eltűnik a víz színén, átkozott a birtokuk az országban, nem fordul a szőlők útjára.
19 Kamar yadda zafi da fări suke shanye ƙanƙarar da ta narke, haka kabari zai ƙwace waɗanda suka yi zunubi. (Sheol )
Szárazság meg hőség elrabolják a hó vízét, az alvilág azokat, kik vétkeztek. (Sheol )
20 Waɗanda suka haife su za su manta da su, tsutsotsi za su cinye su; ba za a sāke tunawa da mugaye ba amma an sare su kamar itace.
Elfelejti őt az anyaméh, édesnek találja a féreg; többé nem emlékeznek rá, s mint a fa, megtöretik a jogtalanság:
21 Suna cutar macen da ba ta da ɗa, suna nuna wa gwauruwa rashin alheri.
a ki kifosztja a magtalan nőt, ki nem szül, s az özveggyel nem tesz jót.
22 Amma Allah cikin ikonsa yakan kawar da masu ƙarfi, ko da yake sun yi ƙarfi, ba su da tabbacin rayuwa.
Ereje által tartós életű a hatalmas, fennmarad, bár nem bízik életében.
23 Mai yiwuwa zai bar su su zauna cikin kwanciyar hankali, amma idanunsa suna kansu.
Megadja neki, hogy bizton támaszkodik, és szemei rajta vannak útjaikon.
24 Sukan samu cin nasara na ɗan lokaci, amma kuma za su ɓace; za su fāɗi a tattara su kamar sauran; za a datse su kamar kan hatsi.
Emelkedtek, kevés még s nincsenek, aláhanyatlottak, mint minden elkapatnak s mint kalász feje levágatnak.
25 “In wannan ba haka ba ne, wane ne zai shaida ƙarya nake yi har yă ƙi yarda da maganata?”
S ha nem így van, ki hazudtol meg engem, hogy semmivé tegye szavamat?